Home Labarai NSCDC ta dauki sabbin matakan tsaro gabanin zaben Gwamnoni

NSCDC ta dauki sabbin matakan tsaro gabanin zaben Gwamnoni

Biyo bayan Nazari gami da rahotannin da suka biyo bayan zaben shugaban kasa da ‘yan majalisar tarayya a Nijeriya a ranar 25 ga watan Fabreru 2023, hukumar tsaro ta  Civil Defence ta tabbatar da tsarin inganta tsaro domin samun nasarar zaben gamnoni da ‘yan majalisun jihohin mai zuwa.

Wannan na kunshe ne ta cikin wata sanarwa da daraktan yada labaran rundunar Olusola Odumosu ya fitar aka kuma raba ga manema labarai a birnin tarayya Abuja.

An tsaurara matakan tsaro domin tabbatar da cewa jami’an hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa INEC sun sami tsaro a lokacin zaben.

Babban kwamandan rundunar Dr. Ahmad Abubakar Audi MNI, OFR ne ya bayyana hakan yayin da yake jawabi ga masu ruwa da tsaki kan zaben gwamnonin da ‘yan majalisun jiha, inda yace sun dauk matakin ne domin magance sake samun matsaloli a inda aka samu da kuma magance faruwar hakan a zabukan dake zuwa.

Ya tabbatar da cewa tuni aka tura jami’ai dubu 102, wadanda aka horar da su yadda ya kamata akan yadda zasu tafikas da yamutsi a taron al’umma yadda ya kamata, sarrafa jama’a da dabarun gudanar da zabe domin tabbatar da tsaro.

Ya kuma tabbatar da cewa jami’an zasu cigaba da aiki da al’ummar kasar domin karbar bayanan sirri domin shawo kan matsalolin da kaje-kazo yayin gudanar da zabe da bayan zaben.

Daga bisani Audi ya bukaci ma’aikatan zabe dasu tabbatar da sunyi aiki yadda ya kamata bisa doka da oda.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp