Home Labarai NSCDC ta dauki sabbin matakan tsaro gabanin zaben Gwamnoni

NSCDC ta dauki sabbin matakan tsaro gabanin zaben Gwamnoni

Biyo bayan Nazari gami da rahotannin da suka biyo bayan zaben shugaban kasa da ‘yan majalisar tarayya a Nijeriya a ranar 25 ga watan Fabreru 2023, hukumar tsaro ta  Civil Defence ta tabbatar da tsarin inganta tsaro domin samun nasarar zaben gamnoni da ‘yan majalisun jihohin mai zuwa.

Wannan na kunshe ne ta cikin wata sanarwa da daraktan yada labaran rundunar Olusola Odumosu ya fitar aka kuma raba ga manema labarai a birnin tarayya Abuja.

An tsaurara matakan tsaro domin tabbatar da cewa jami’an hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa INEC sun sami tsaro a lokacin zaben.

Babban kwamandan rundunar Dr. Ahmad Abubakar Audi MNI, OFR ne ya bayyana hakan yayin da yake jawabi ga masu ruwa da tsaki kan zaben gwamnonin da ‘yan majalisun jiha, inda yace sun dauk matakin ne domin magance sake samun matsaloli a inda aka samu da kuma magance faruwar hakan a zabukan dake zuwa.

Ya tabbatar da cewa tuni aka tura jami’ai dubu 102, wadanda aka horar da su yadda ya kamata akan yadda zasu tafikas da yamutsi a taron al’umma yadda ya kamata, sarrafa jama’a da dabarun gudanar da zabe domin tabbatar da tsaro.

Ya kuma tabbatar da cewa jami’an zasu cigaba da aiki da al’ummar kasar domin karbar bayanan sirri domin shawo kan matsalolin da kaje-kazo yayin gudanar da zabe da bayan zaben.

Daga bisani Audi ya bukaci ma’aikatan zabe dasu tabbatar da sunyi aiki yadda ya kamata bisa doka da oda.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp