Home Labarai NSCDC ta dauki sabbin matakan tsaro gabanin zaben Gwamnoni

NSCDC ta dauki sabbin matakan tsaro gabanin zaben Gwamnoni

Biyo bayan Nazari gami da rahotannin da suka biyo bayan zaben shugaban kasa da ‘yan majalisar tarayya a Nijeriya a ranar 25 ga watan Fabreru 2023, hukumar tsaro ta  Civil Defence ta tabbatar da tsarin inganta tsaro domin samun nasarar zaben gamnoni da ‘yan majalisun jihohin mai zuwa.

Wannan na kunshe ne ta cikin wata sanarwa da daraktan yada labaran rundunar Olusola Odumosu ya fitar aka kuma raba ga manema labarai a birnin tarayya Abuja.

An tsaurara matakan tsaro domin tabbatar da cewa jami’an hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa INEC sun sami tsaro a lokacin zaben.

Babban kwamandan rundunar Dr. Ahmad Abubakar Audi MNI, OFR ne ya bayyana hakan yayin da yake jawabi ga masu ruwa da tsaki kan zaben gwamnonin da ‘yan majalisun jiha, inda yace sun dauk matakin ne domin magance sake samun matsaloli a inda aka samu da kuma magance faruwar hakan a zabukan dake zuwa.

Ya tabbatar da cewa tuni aka tura jami’ai dubu 102, wadanda aka horar da su yadda ya kamata akan yadda zasu tafikas da yamutsi a taron al’umma yadda ya kamata, sarrafa jama’a da dabarun gudanar da zabe domin tabbatar da tsaro.

Ya kuma tabbatar da cewa jami’an zasu cigaba da aiki da al’ummar kasar domin karbar bayanan sirri domin shawo kan matsalolin da kaje-kazo yayin gudanar da zabe da bayan zaben.

Daga bisani Audi ya bukaci ma’aikatan zabe dasu tabbatar da sunyi aiki yadda ya kamata bisa doka da oda.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp