Home Labarai NNPP ta zargi DSS da hada baki da Gwamnatin Jihar Kano

NNPP ta zargi DSS da hada baki da Gwamnatin Jihar Kano

Babbar jam’iyya adawa ta NNPP a jihar kano ta zargi daraktan DSS da hada baki da gwamnatin APC a jihar domin yin magudin zabe.

Jigo a jam’iyya kuma guda cikin ‘yan takarar sanata a shiyyar kano ta Arewa a zaben shekarar 2023 Dr. Baffa Bichi ne ya bayyana hakan yayin da yake ganawa da manema labarai a yammacin ranar laraba.

Haka kuma jam’iyyar ta zargi hukumar tsaro ta farin kaya da karawa daraktan hukumar wa’adin aiki kasancewar tuni ya zarta lokacin da doka ta tanadawa ma’aikacin gwamnati ya dauka wato dai shekaru yin ritayar sa.

A don haka jam’iyyar ta NNPP ta shirya gudanar da zanga -zangar lumana a ranar Alhamis 16 ga watan Maris 2023 a kan titin Kano Club dake jihar kano.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp