Home General Mutune 5 sun mutu a wata arangama tsakani Mabiya Shi’a da Jami’an...

Mutune 5 sun mutu a wata arangama tsakani Mabiya Shi’a da Jami’an Tsaro

Musulmi mabiya darikar shi’a sun zargi gwamnan jihar Kaduna, malam Nasiru El’rufa’I da hallaka mabiya darikar mutum biyar.

‘Yan shi’ar sun zargi jami’an tsaron gwamnan da bude wuta kan mutanen yayin da suke gudanar da zanga-zanga a jihar kaduna ranar alhamis.

Wannan na kunshe ta cikin wata sanarwa da sakataren harkokin ilimi na kungiyar Abdullahi Musa ya fita.

Haka kuma kungiyar tayi zargin lamarin nada alaka da kalaman tunzuri da Gwamnan yayi kwanaki kadan da suka gabata.

An ruwaito cewa mutane da dama sun sami raunika cikin su harda wadanda ke tafiya a gefen hanya yayin da lamarin ya auku.

Sanarwa ta kara da cewa “kwanaki kadan da suka gabata ne gwaman jihar kaduna, Malam Nasiru El’rufa’i, yayi wasu kalamai domin tunzura ‘ya’yan jam’iyyar sa a zariya akan mabiyar darikar shi’a da shugabanta Sheik Ibrahim Zakzaky (H), inda ya shaida cewa dole ne su zabi dan takarar sa Sanata Uba Sani domin ya gama da ragowar ‘yan shi’ar da suka rage a garin na zari’a.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp