Home General Mutune 5 sun mutu a wata arangama tsakani Mabiya Shi’a da Jami’an...

Mutune 5 sun mutu a wata arangama tsakani Mabiya Shi’a da Jami’an Tsaro

Musulmi mabiya darikar shi’a sun zargi gwamnan jihar Kaduna, malam Nasiru El’rufa’I da hallaka mabiya darikar mutum biyar.

‘Yan shi’ar sun zargi jami’an tsaron gwamnan da bude wuta kan mutanen yayin da suke gudanar da zanga-zanga a jihar kaduna ranar alhamis.

Wannan na kunshe ta cikin wata sanarwa da sakataren harkokin ilimi na kungiyar Abdullahi Musa ya fita.

Haka kuma kungiyar tayi zargin lamarin nada alaka da kalaman tunzuri da Gwamnan yayi kwanaki kadan da suka gabata.

An ruwaito cewa mutane da dama sun sami raunika cikin su harda wadanda ke tafiya a gefen hanya yayin da lamarin ya auku.

Sanarwa ta kara da cewa “kwanaki kadan da suka gabata ne gwaman jihar kaduna, Malam Nasiru El’rufa’i, yayi wasu kalamai domin tunzura ‘ya’yan jam’iyyar sa a zariya akan mabiyar darikar shi’a da shugabanta Sheik Ibrahim Zakzaky (H), inda ya shaida cewa dole ne su zabi dan takarar sa Sanata Uba Sani domin ya gama da ragowar ‘yan shi’ar da suka rage a garin na zari’a.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp