Home General Mutune 5 sun mutu a wata arangama tsakani Mabiya Shi’a da Jami’an...

Mutune 5 sun mutu a wata arangama tsakani Mabiya Shi’a da Jami’an Tsaro

Musulmi mabiya darikar shi’a sun zargi gwamnan jihar Kaduna, malam Nasiru El’rufa’I da hallaka mabiya darikar mutum biyar.

‘Yan shi’ar sun zargi jami’an tsaron gwamnan da bude wuta kan mutanen yayin da suke gudanar da zanga-zanga a jihar kaduna ranar alhamis.

Wannan na kunshe ta cikin wata sanarwa da sakataren harkokin ilimi na kungiyar Abdullahi Musa ya fita.

Haka kuma kungiyar tayi zargin lamarin nada alaka da kalaman tunzuri da Gwamnan yayi kwanaki kadan da suka gabata.

An ruwaito cewa mutane da dama sun sami raunika cikin su harda wadanda ke tafiya a gefen hanya yayin da lamarin ya auku.

Sanarwa ta kara da cewa “kwanaki kadan da suka gabata ne gwaman jihar kaduna, Malam Nasiru El’rufa’i, yayi wasu kalamai domin tunzura ‘ya’yan jam’iyyar sa a zariya akan mabiyar darikar shi’a da shugabanta Sheik Ibrahim Zakzaky (H), inda ya shaida cewa dole ne su zabi dan takarar sa Sanata Uba Sani domin ya gama da ragowar ‘yan shi’ar da suka rage a garin na zari’a.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp