Home General Mutune 5 sun mutu a wata arangama tsakani Mabiya Shi’a da Jami’an...

Mutune 5 sun mutu a wata arangama tsakani Mabiya Shi’a da Jami’an Tsaro

Musulmi mabiya darikar shi’a sun zargi gwamnan jihar Kaduna, malam Nasiru El’rufa’I da hallaka mabiya darikar mutum biyar.

‘Yan shi’ar sun zargi jami’an tsaron gwamnan da bude wuta kan mutanen yayin da suke gudanar da zanga-zanga a jihar kaduna ranar alhamis.

Wannan na kunshe ta cikin wata sanarwa da sakataren harkokin ilimi na kungiyar Abdullahi Musa ya fita.

Haka kuma kungiyar tayi zargin lamarin nada alaka da kalaman tunzuri da Gwamnan yayi kwanaki kadan da suka gabata.

An ruwaito cewa mutane da dama sun sami raunika cikin su harda wadanda ke tafiya a gefen hanya yayin da lamarin ya auku.

Sanarwa ta kara da cewa “kwanaki kadan da suka gabata ne gwaman jihar kaduna, Malam Nasiru El’rufa’i, yayi wasu kalamai domin tunzura ‘ya’yan jam’iyyar sa a zariya akan mabiyar darikar shi’a da shugabanta Sheik Ibrahim Zakzaky (H), inda ya shaida cewa dole ne su zabi dan takarar sa Sanata Uba Sani domin ya gama da ragowar ‘yan shi’ar da suka rage a garin na zari’a.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp