Home DUNIYA Mayakan M23 sun fara janyewa daga yankunan da suka kwace a Congo

Mayakan M23 sun fara janyewa daga yankunan da suka kwace a Congo

Rahotanni daga Jamhuriyyar Demokradiyyar Congo na cewa mayakan ‘yan tawayen M23 sun fara janyewa daga yankunan da suka kwace iko da su a gabashin kasar, matakin da ke zuwa bayan jibge karin dakarun kasashen ketare a yankin.

Majiyoyin Soji da na fararen hula sun tabbatarwa Kamfanin Dillancin Labarai na AFP batun janyewar mayakan na M23 wadanda a baya suka kwace garuruwa da dama a lardin na arewacin Kivu da ke gabashin kasar bayan gwabza yaki na tsawon watanni tsakaninsu da dakarun gwamnatin Congo.

Shugaban mayakan sa kai na garin Mweso da ke yankin Masisi mai tazarar kilomita 100 da birnin Goma fadar gwamnatin lardin na Kivu, Alphonse Habinna ya shaidawa AFP ta wayar tarho cewa basu da masaniya kan dalilin janyewar dakarun.

Sai dai duk da wannan janyewa, Mayakan na M23 na kuma ci gaba da gwabza fada tsakaninsu da dakarun Congo wadanda ke samun taimakon sojojin kasashen gabashin Afrika 7 a yankuna da dama bayan lardin na Kivu.

Duk da shiga tsakanin da Rwanda ta yi wanda ya kai ga kulla yarjejeniyar tsagaita wuta, bangarorin biyu sun koma kai wa juna farmaki kasa da mako guda bayan cimmajituwar a ranar 7 ga watan nan, inda a baya-bayan nan M23 ta yi barazanar katse hanyar da ta hada iyakokin Congo da Rwanda bayan karakarfin da sukayi a gab da birnin Goma.

Wannan mataki na M23 na zuwa ne a daidai lokacin da jami’na diflomasiyya ke tsaka da tattaunawa a kokarin kawo karshen yankin na tsawon shekara guda da ya tagayyara tarin iyalai.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp