Home DUNIYA Mayakan M23 sun fara janyewa daga yankunan da suka kwace a Congo

Mayakan M23 sun fara janyewa daga yankunan da suka kwace a Congo

Rahotanni daga Jamhuriyyar Demokradiyyar Congo na cewa mayakan ‘yan tawayen M23 sun fara janyewa daga yankunan da suka kwace iko da su a gabashin kasar, matakin da ke zuwa bayan jibge karin dakarun kasashen ketare a yankin.

Majiyoyin Soji da na fararen hula sun tabbatarwa Kamfanin Dillancin Labarai na AFP batun janyewar mayakan na M23 wadanda a baya suka kwace garuruwa da dama a lardin na arewacin Kivu da ke gabashin kasar bayan gwabza yaki na tsawon watanni tsakaninsu da dakarun gwamnatin Congo.

Shugaban mayakan sa kai na garin Mweso da ke yankin Masisi mai tazarar kilomita 100 da birnin Goma fadar gwamnatin lardin na Kivu, Alphonse Habinna ya shaidawa AFP ta wayar tarho cewa basu da masaniya kan dalilin janyewar dakarun.

Sai dai duk da wannan janyewa, Mayakan na M23 na kuma ci gaba da gwabza fada tsakaninsu da dakarun Congo wadanda ke samun taimakon sojojin kasashen gabashin Afrika 7 a yankuna da dama bayan lardin na Kivu.

Duk da shiga tsakanin da Rwanda ta yi wanda ya kai ga kulla yarjejeniyar tsagaita wuta, bangarorin biyu sun koma kai wa juna farmaki kasa da mako guda bayan cimmajituwar a ranar 7 ga watan nan, inda a baya-bayan nan M23 ta yi barazanar katse hanyar da ta hada iyakokin Congo da Rwanda bayan karakarfin da sukayi a gab da birnin Goma.

Wannan mataki na M23 na zuwa ne a daidai lokacin da jami’na diflomasiyya ke tsaka da tattaunawa a kokarin kawo karshen yankin na tsawon shekara guda da ya tagayyara tarin iyalai.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp