Home DUNIYA Mayakan M23 sun fara janyewa daga yankunan da suka kwace a Congo

Mayakan M23 sun fara janyewa daga yankunan da suka kwace a Congo

Rahotanni daga Jamhuriyyar Demokradiyyar Congo na cewa mayakan ‘yan tawayen M23 sun fara janyewa daga yankunan da suka kwace iko da su a gabashin kasar, matakin da ke zuwa bayan jibge karin dakarun kasashen ketare a yankin.

Majiyoyin Soji da na fararen hula sun tabbatarwa Kamfanin Dillancin Labarai na AFP batun janyewar mayakan na M23 wadanda a baya suka kwace garuruwa da dama a lardin na arewacin Kivu da ke gabashin kasar bayan gwabza yaki na tsawon watanni tsakaninsu da dakarun gwamnatin Congo.

Shugaban mayakan sa kai na garin Mweso da ke yankin Masisi mai tazarar kilomita 100 da birnin Goma fadar gwamnatin lardin na Kivu, Alphonse Habinna ya shaidawa AFP ta wayar tarho cewa basu da masaniya kan dalilin janyewar dakarun.

Sai dai duk da wannan janyewa, Mayakan na M23 na kuma ci gaba da gwabza fada tsakaninsu da dakarun Congo wadanda ke samun taimakon sojojin kasashen gabashin Afrika 7 a yankuna da dama bayan lardin na Kivu.

Duk da shiga tsakanin da Rwanda ta yi wanda ya kai ga kulla yarjejeniyar tsagaita wuta, bangarorin biyu sun koma kai wa juna farmaki kasa da mako guda bayan cimmajituwar a ranar 7 ga watan nan, inda a baya-bayan nan M23 ta yi barazanar katse hanyar da ta hada iyakokin Congo da Rwanda bayan karakarfin da sukayi a gab da birnin Goma.

Wannan mataki na M23 na zuwa ne a daidai lokacin da jami’na diflomasiyya ke tsaka da tattaunawa a kokarin kawo karshen yankin na tsawon shekara guda da ya tagayyara tarin iyalai.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp