Home Labarai Gwamnatin Buhari na shirin cire tallafin Man Fetur

Gwamnatin Buhari na shirin cire tallafin Man Fetur

Gwamnatin Najeriya ta ce ta na shirin kammala cire tallafin man fetur kafin mika mulki ga sabuwar gwamnati a ranar 29 ga watan Mayun wannan shekara.

Ministar kudi da tsare tsaren kasar Zainab Shamsuna Ahmed ta bayyana shirin a Abuja, inda ta ke cewa shirin cire tallafin shi ne wanda jama’a basa so amma kuma ya zama wajibi, a dai dai lokacin da akasarin ‘yan Najeriya suka yarda cewar tallafin baya taimakon talaka.

Ahmed ta ce sun samu umurnin cire tallafin nan da watan Yuni na wannan shekara kamar yadda majalisa ta amince da shi a cikin kasafin kudin wannan shekara, kuma za su aiwatar da shi domin bai wa kasuwa damar samar da farashin a koda yaushe.

Ministar ta ce idan an cire tallafin, zai ba iwa ‘yan kasuwa da masu zuba jari damar shiga harkokin kasuwancin man da kuma samar da shi ga jama’a.

Zainab Ahmed ta ce kawo karshen zuba tallafin man zai bai wa gwamnati damar karkata kudin da ake sanyawa zuwa bangarori da dama da suka hada da inganta asibitoci da makarantu da kuma samar da kayan more rayuwa.

Ministar ta bukaci ‘yan Najeriya da su goyawa gwamnatin baya wajen ganin an kawo karshen wannan tallafi wanda ke amfana wasu mutane ‘yan kadan.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
https://nnn.ng/image-compressor/
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp