Home Labarai Makiyaya sun hallaka mutane sama da dubu 5 a jihar Benue –...

Makiyaya sun hallaka mutane sama da dubu 5 a jihar Benue – BSEMA

Wani rahoto da hukumar bayar da agajin gaggawa ta jihar Benewai (BSEMA) ta fitar ya bayyana cewa wasu da ake zargin makiyaya ne sun hallaka kimanin mutane 5,138 a wasu kauyukan jihar tun daga shekarar 2015.

Babban sakataren hukumar, Dakta Emmanuel Shior, ne ya bayyana hakan a garin Makurdi yayin da yake ganawa da manema labarai, ya kuma yi zargin cewa wasu mutane dubu 3 sun rasa muhallansu sakamakon hare-haren da makiyayan suka kai a kwanakin baya a kananan hukumomin Gwer ta yamma, Logo, Ukum da kwande yayin da suka murna bisa faduwar da gwamnan Samuel Ortom jihar yayi a takarar sanata.

Ya ce a kalla kananan hukumomi 18 cikin 23 dake jihar makiyayan suka yiwa kawanya tare da kone gidaje, abinda ya jefa mutane miliyan 2 cikin halin rashin matsugunni.

Shugaban hukumar ta BSEMA yace ya karanta a jaridu cewa kungiyar Fulani na Shirin daukar wasu matakan akan jihar, inda yace yana mai bayyana fatan cewa gwamnatin Benuwai ba za ta yi kasa a gwiwa ba saboda rashin goyon bayan gwamnatin tarayya da kuma dan takarar gwamna a jam’iyyar PDP, Titus Uba, ba zai  sauya matakin da Gwamna Samuel Ortom ya yi na tallafawa ‘yan gudun hijira a jihar ba.

Shior ya dage cewa sama da ‘yan gudun hijirar Kamaru 10,000 a karamar hukumar Kwande da ke jihar suna samun kariya daga jami’an sa kai na al’ummar jihar Benuwe daga farmakin makiyaya.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp