Home Labarai Makiyaya sun hallaka mutane sama da dubu 5 a jihar Benue –...

Makiyaya sun hallaka mutane sama da dubu 5 a jihar Benue – BSEMA

Wani rahoto da hukumar bayar da agajin gaggawa ta jihar Benewai (BSEMA) ta fitar ya bayyana cewa wasu da ake zargin makiyaya ne sun hallaka kimanin mutane 5,138 a wasu kauyukan jihar tun daga shekarar 2015.

Babban sakataren hukumar, Dakta Emmanuel Shior, ne ya bayyana hakan a garin Makurdi yayin da yake ganawa da manema labarai, ya kuma yi zargin cewa wasu mutane dubu 3 sun rasa muhallansu sakamakon hare-haren da makiyayan suka kai a kwanakin baya a kananan hukumomin Gwer ta yamma, Logo, Ukum da kwande yayin da suka murna bisa faduwar da gwamnan Samuel Ortom jihar yayi a takarar sanata.

Ya ce a kalla kananan hukumomi 18 cikin 23 dake jihar makiyayan suka yiwa kawanya tare da kone gidaje, abinda ya jefa mutane miliyan 2 cikin halin rashin matsugunni.

Shugaban hukumar ta BSEMA yace ya karanta a jaridu cewa kungiyar Fulani na Shirin daukar wasu matakan akan jihar, inda yace yana mai bayyana fatan cewa gwamnatin Benuwai ba za ta yi kasa a gwiwa ba saboda rashin goyon bayan gwamnatin tarayya da kuma dan takarar gwamna a jam’iyyar PDP, Titus Uba, ba zai  sauya matakin da Gwamna Samuel Ortom ya yi na tallafawa ‘yan gudun hijira a jihar ba.

Shior ya dage cewa sama da ‘yan gudun hijirar Kamaru 10,000 a karamar hukumar Kwande da ke jihar suna samun kariya daga jami’an sa kai na al’ummar jihar Benuwe daga farmakin makiyaya.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp