Home Labarai NBC ta sanyawa wasu kafafen yada labarai 25 takunkumi sakamakon karya dokoki

NBC ta sanyawa wasu kafafen yada labarai 25 takunkumi sakamakon karya dokoki

Hukumar dake lura da kafafen yada labarai ta Najeriya NBC ta sanyawa wasu kafafen yada labarai 25 takunkumi sakamakon karya dokokin hukumar a lokacin zaben shugaban kasa da na ‘yan majalisun tarayya.

Daraktan hukumar na kasa Balarabe Shehu Illele ne ya bayyana hakan a ranar Laraba yayin da yake zantawa da manema labarai, inda ya kara da cewa hukumar ta kuma baiwa wasu kafafen yada labarai 16 gargadi domin su gyara ayyukansu.

Ya kara da cewa wasu daga cikin wadannan kafafen yada labaran sun baiwa baki da masu fashin baki har ma da masu kiran waya a yayin shirye-shirye damar furta wasu kalmomi mara sa da dadi ba tare da yi musu linzami ba.

Balarabe Illela ya kuma bukaci sauran kafafen yada labaran kasar da su mayar da hankali wajen sanya kwarewa da kuma bin doka da oda yayin gudanar da ayyukansu.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp