Home Labarai An samu karin mutane 142 da zazzabin Lassa ya hallaka a Najeriya

An samu karin mutane 142 da zazzabin Lassa ya hallaka a Najeriya

Hukumar dakile cutuka masu yaduwa ta Najeriya, ta ce cikin kasa da watanni uku, an samu rahoton mutane 784 da suka kamu da zazzabin Lassa, inda mutum 142 suka mutu a jihohin kasar 23.

Hukumar ta bayyana hakan ne a shafinta na yanar gizo, inda ta ce an samu rahoton mutanen da suka kamu da cutar ne, daga watan Janairun 2023 zuwa yanzu.

Haka kuma an samu rahoton bullar cutar ne a jihohin Edo, Ondo, Ebonyi, Bauchi, Taraba, Benue, Rivers, Plateau, da kuma Nasarawa.

NCDC ta ce a jimilla daga mako na 1 zuwa mako na 11, a 2023, an samu rahoton mutuwar mutane 142 daidai da kashi 18.1 cikin 100 wanda ya yi kasa da kashi 18.7 na shekarar 2022.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Dangote ya ƙara farashin man feturHukumar Jin dadin alhazan Kano ta sanar da ranar fara jigilar maniyatantaYadda Lakurawa suka kashe masallata a KebbiDSS ta kama jagoran ISWAP da ake nema ruwa a jallo a EdoBa mu taɓa goyon bayan musguna wa Kristoci ba - Gwamnatin NajeriyaGobara ta tashi a babban kasuwar Fika da ke jihar YobeWaye Tunji Disu: Sabon Babban Sifeton 'Yansandan NajeriyaNijar ta amince da kundin ayyukan AES na shekara ta biyuAtiku ya zargi gwamnatin Tinubu da yi wa dimokuraɗiyya zagon ƙasaGwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanci
X whatsapp