Home Labarai DSS ta tabbatar da maƙarƙashiyar kafa gwamnatin riƙo a Najeriya

DSS ta tabbatar da maƙarƙashiyar kafa gwamnatin riƙo a Najeriya

Hukumar tsaro ta farin kaya a Najeriya ta ce ta shaida wasu jiga-jigai a wata maƙarƙashiya ake kitsawa don kafa gwamnatin riƙon ƙwarya a ƙasar.

Hukumar ta ce maƙarƙashiyar, wanda wasu ke izawa ba kawai abu ne da ya saɓa wa doka ba, wani ƙoƙarin masu jamhuru ne na kifar da tsarin mulkin Najeriya da kuma jefa ƙasar cikin wani rikici da za a iya kaucewa.

Ta ce tunanin kafa gwamnatin riƙon ƙwarya, abu ne da ba za a amince da shi ba a tsarin dimokraɗiyya da kuma zaman lafiyar al’ummar ƙasar.

A saƙon da ta wallafa a shafinta na Tuwita ɗauke da sa hannun jami’in yaɗa labaran hukumar, Peter Afunanya, DSS ta ce tun bayan zaɓukan ƙasar da aka kammala cikin kwanciyar hankali, ake ta raɗe-raɗin kafa gwamnatin riƙo.

Sai dai DSS ba ta fito kai tsaye ta ce ga ‘yan siyasar da take zargi da shirya wannan maƙarƙashiya ba.

Ta dai ce masu kitsa makircin, a jerin tarukan da suke yi, suna auna batutuwa da dama a ciki har da yadda za su ɗauki nauyin zanga-zanga maras iyaka a manyan birane ta yadda daga bisani za a ayyana dokar ta-ɓaci.

Wani abin kuma shi ne, su samu umarnin kotu don hana rantsar da sabbin shugabanni da ƴan majalisa a matakin tarayya da jihohi.

‘Yan adawa a Najeriya sun soki lamirin sakamakon zaɓen shugaban ƙasa wanda ya bai wa Bola Ahmed Tinubu nasara a watan Fabrairun 2023. Sun yi zargin cewa zaɓen yana cike da kura-kurai, kuma an tafka maguɗi, baya ga amfani da tashe-tashen hankula don yin tarnaƙi ga zaɓen 25 ga watan Fabrairu.

Haka zalika, manyan ‘yan adawan da suka yi takara da Bola Ahmed Tinubu kamar Atiku Abubakar na jam’iyyar PDP da Peter Obi na Labour Party duk sun shigar da ƙara a gaban kotun sauraron ƙorafe-ƙorafen zaɓe don ƙalubalantar nasarar Tinubu.

Ita dai Hukumar DSS ta bayyana goyon baya ga ƙudurin Shugaba Buhari na tabbatar da ganin an miƙa mulki ba tare da wani tashin hankali ba, kuma ta ce za ta yi aiki tuƙuru don ganin tabbatar hakan.

Ta kuma ce tana goyon bayan kwamitocin miƙa mulki da shugaban ƙasar ya kafa da kuma waɗanda aka kafa a jihohi.

Hukumar ta ƙara da cewa za ta yi aiki da sauran hukumomin tsaro don ganin an yi bikin miƙa mulki a ranar 29 ga watan Mayun 2023.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp