Home SIYASA Gawuna ya yi wa Abba Gida-Gida fatan alheri a mulkin Kano

Gawuna ya yi wa Abba Gida-Gida fatan alheri a mulkin Kano

Mataimakin gwamnan Kano kuma ɗan takarar jam’iyyar APC a zaɓen gwamnan jihar, Nasir Yusuf Gawuna ya yi wa zaɓaɓɓen gwamnan jihar, Abba Kabir Yusuf addu’ar samun nasara a mulkinsa tare da yi wa kansa da magoya bayan jam’iyyar APC fatan ɗaukar kaddara.

Gawuna ya bayyana hakan ne a cikin wani saƙon murya da aka naɗa, wadda aka rabawa manema labarai a jihar kano.

Matakin na zuwa ne jim kaɗan bayan Hukumar Zaɓe mai Zaman Kanta ta Najeriya (INEC) ta bai wa Abba Gida-Gida takardar shaidar cin zaɓen gwamna a ranar Laraba.

A cikin saƙon, Nasir Gawuna ya ce “shi (Abba) wanda Allah Ya bai wa, Allah Ya sa ya zama shugaba nagari, mai adalci ga kowa.”

Ya ƙara da cewa “Mu kuma Allah Ya sa mu zama masu biyayya ga shugabanci da kuma bin doka.”

Gawuna ya buƙaci magoya bayansa su ƙara haƙuri tare da addu’ar ɗaukan kadara a rashin nasarar da jam’iyyar ta yi a zaɓen gwamna na shekarar 2023.

A ranar 20 ga watan Mayu ne, INEC ta bayyana Abba Kabir Yusuf a matsayin wanda ya lashe zaɓen gwamnan jihar Kano bayan zaɓen da aka yi ranar 18 ga watan na Mayu.

Babban jami’in tattara sakamakon zaɓen gwamnan Kano Farfesa Ahmad Doko Ibrahim ya ce Abba Kabir ya samu ƙuri’u 1,019,602, yayin da Nasiru Gawuna ya samu ƙuri’u 890,705.

Sai dai jam’iyyar APC ta ce ba ta yarda da sakamakon ba, kuma ta buƙaci INEC ta sake nazari kan zaɓen.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp