An Samu sabbin wadanda suka kamu da Corona 5 a jihohi 2 na Nijeriya

Hukumar yaki da cutuka masu yaduwa ta NCDC a Najeriya ta sanar da samun akalla mutane 5 da suka harbu da cutar corona a sassan kasar daga ranar 25 ga watan Fabarairu zuwa 31 ga watan Maris din da ya gabata.

Alkaluman da hukumar ta fitar a yau asabar sun nuna cewa sabbin kamuwa da cutar sun fito ne daga jihohin Lagos da Rivers wadanda kuma tuni aka killace su don dakile yaduwar cutar.

NCDC ta bayyana cewa mutum 4 suka harbu da cutar a jihar Lagos yayinda wani 1 ya harbu da ita a Rivers, lamarin da ke sanya fargabar yiwuwar dawowa da kuma fantsamuwar cutar a sassan Najeriya.

Zuwa yanzu alkaluman NCDC na nuna cewa mutum dubu 266 da 665 suka harbu da cutar Covid-19 a Najeriyar tun daga lokacin da aka samu bullar cutar zuwa yanzu.

A cewar NCDC cikin jumullar wadanda suka kamu da cutar covid-19 a Najeriya mutum subu 259 da 951 sun samu warkewa yayinda cutar ta kashe mutum dubu 3 da 155 a jihohin kasar 36 da birnin Abuja.

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1190 days 9 hours 27 minutes 42 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1172 days 11 hours 9 minutes 7 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com