Home General Tun bayan yaƙin basasa, Najeriya bata ta ba fuskantar rarrabuwar kawuna kamar...

Tun bayan yaƙin basasa, Najeriya bata ta ba fuskantar rarrabuwar kawuna kamar yanzu ba – Sanusi Lamido Sunusi

Khalifan Tijjaniyya, Muhammadu Sanusi II ya yi gargaɗi cewa Najeriya ta fi fama da rarrabuwar kai saboda ƙabilanci da bambancin addini tun bayan yaƙin Biafra fiye da shekara 50 da ta wuce.

Da yake jawabi a wani taro a Legas, Muhammadu Sanusi wanda ya ce “ba na tunanin Najeriya ta taɓa kasancewa a mawuyacin yanayi kamar yanzu tun bayan yaƙin basasa. Muna da ƙalubale game da aikin gina ƙasar nan.

Ya ce Najeriya tana fama da bambance-bambancen addini da na ƙabilanci.

“Muna da tattalin arzikin da ke fuskantar taɓarɓarewa kuma abin takaici, da alama muna fama da ƙarancin shugabanci na gari.”

Kalaman tsohon gwamnan CBN ɗin na zuwa ne yayin da Shugaba Muhammadu Buhari ke shirye-shiryen miƙa mulki ga Bola Tinubu.

Tinubu ne ya yi nasara a kan manyan abokan takararsa – Atiku Abubakar da Peter Obi a zaɓen shugaban ƙasar mai zafi da aka yi a watan Fabrairu.

Atiku da Obi sun yi fatali da sakamakon zaɓen, kuma tuni suka shigar da ƙara a kotu

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp