Home Labarai An Samu sabbin wadanda suka kamu da Corona 5 a jihohi 2...

An Samu sabbin wadanda suka kamu da Corona 5 a jihohi 2 na Nijeriya

Hukumar yaki da cutuka masu yaduwa ta NCDC a Najeriya ta sanar da samun akalla mutane 5 da suka harbu da cutar corona a sassan kasar daga ranar 25 ga watan Fabarairu zuwa 31 ga watan Maris din da ya gabata.

Alkaluman da hukumar ta fitar a yau asabar sun nuna cewa sabbin kamuwa da cutar sun fito ne daga jihohin Lagos da Rivers wadanda kuma tuni aka killace su don dakile yaduwar cutar.

NCDC ta bayyana cewa mutum 4 suka harbu da cutar a jihar Lagos yayinda wani 1 ya harbu da ita a Rivers, lamarin da ke sanya fargabar yiwuwar dawowa da kuma fantsamuwar cutar a sassan Najeriya.

Zuwa yanzu alkaluman NCDC na nuna cewa mutum dubu 266 da 665 suka harbu da cutar Covid-19 a Najeriyar tun daga lokacin da aka samu bullar cutar zuwa yanzu.

A cewar NCDC cikin jumullar wadanda suka kamu da cutar covid-19 a Najeriya mutum subu 259 da 951 sun samu warkewa yayinda cutar ta kashe mutum dubu 3 da 155 a jihohin kasar 36 da birnin Abuja.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp