Home Labarai ‘Yan bindiga sun sace dalibai mata biyu na jami’ar Gusau

‘Yan bindiga sun sace dalibai mata biyu na jami’ar Gusau

‘Yan bindiga sun sace ɗalibai mata guda biyu a jami’ar tarayya da ke Gusau a jihar Zamfara, arewa maso yammacin Najeriya.

Rahotonni sun ce ‘yan fashin ɗauke da muggan makamai, sun sace ɗaliban ne a ɗakunan kwanansu da ke wajen makarantar.

Wata sanarwa da rundunar ‘yan sandan jihar ta fitar, ta ambato kwamishinan ‘yan sandan Zamfara, CP Kolo Yusuf na tabbatar wa iyayen ɗaliban da kuma hukumar makarantar cewa rundunar tana ƙoƙari don ganin ta kuɓutar da su.

Ta ce ‘yan sanda sun samu rahoton sace ɗaliban a ɗakunan kwanansu da ke a wajen makarantar, kuma ba ta yi ƙasa a gwiwa ba, ta tura jami’anta zuwa wajen da lamarin ya auku.

Sai dai kafin zuwan jami’an tsaron ‘yan fashin sun tsere da ɗaliban, kamar yadda sanarwar ta bayyana.

Haka kuma sanarwar ta ce kwamishinan ‘yan sandan ya tura ƙarin jami’an tsaro don bin sawun ‘yan fashin da kuma kuɓutar da ɗaliban.

Zamfara, ta yi ƙaurin suna a matsayin jihar da ‘yan fashin daji suka mamaye wasu sassanta, inda suke kai hare-hare da sace mutane a ciki har wajen jihar suna neman kuɗin fansa daga makusanta da dangin waɗanda abin ya ritsa da su.

An yi imani har yanzu akwai ragowar daliban kwalejin tarayya ta Yawuri kimanin 11 dukkansu mata, waɗanda aka sato daga jihar Kebbi mai maƙwabtaka, kuma ake ci gaba da tsarewa a wani daji da ke cikin Zamfara wanda a yanzu sun kwashe kwanan 653.

Ranar 16 ga watan Yunin 2021 ne, ‘yan bindigar suka sace ɗaliban su kimanin 100 tare da wasu malamansu, inda suka tafi da su daji, kafin daga bisani su saki mafi yawansu cikin rukuni-rukuni.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp