Home Labarai ‘Yan bindiga sun sace dalibai mata biyu na jami’ar Gusau

‘Yan bindiga sun sace dalibai mata biyu na jami’ar Gusau

‘Yan bindiga sun sace ɗalibai mata guda biyu a jami’ar tarayya da ke Gusau a jihar Zamfara, arewa maso yammacin Najeriya.

Rahotonni sun ce ‘yan fashin ɗauke da muggan makamai, sun sace ɗaliban ne a ɗakunan kwanansu da ke wajen makarantar.

Wata sanarwa da rundunar ‘yan sandan jihar ta fitar, ta ambato kwamishinan ‘yan sandan Zamfara, CP Kolo Yusuf na tabbatar wa iyayen ɗaliban da kuma hukumar makarantar cewa rundunar tana ƙoƙari don ganin ta kuɓutar da su.

Ta ce ‘yan sanda sun samu rahoton sace ɗaliban a ɗakunan kwanansu da ke a wajen makarantar, kuma ba ta yi ƙasa a gwiwa ba, ta tura jami’anta zuwa wajen da lamarin ya auku.

Sai dai kafin zuwan jami’an tsaron ‘yan fashin sun tsere da ɗaliban, kamar yadda sanarwar ta bayyana.

Haka kuma sanarwar ta ce kwamishinan ‘yan sandan ya tura ƙarin jami’an tsaro don bin sawun ‘yan fashin da kuma kuɓutar da ɗaliban.

Zamfara, ta yi ƙaurin suna a matsayin jihar da ‘yan fashin daji suka mamaye wasu sassanta, inda suke kai hare-hare da sace mutane a ciki har wajen jihar suna neman kuɗin fansa daga makusanta da dangin waɗanda abin ya ritsa da su.

An yi imani har yanzu akwai ragowar daliban kwalejin tarayya ta Yawuri kimanin 11 dukkansu mata, waɗanda aka sato daga jihar Kebbi mai maƙwabtaka, kuma ake ci gaba da tsarewa a wani daji da ke cikin Zamfara wanda a yanzu sun kwashe kwanan 653.

Ranar 16 ga watan Yunin 2021 ne, ‘yan bindigar suka sace ɗaliban su kimanin 100 tare da wasu malamansu, inda suka tafi da su daji, kafin daga bisani su saki mafi yawansu cikin rukuni-rukuni.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp