Home Labarai NBC ta ci tarar Tashar Channels Miliyan 5

NBC ta ci tarar Tashar Channels Miliyan 5

Hukumar dake lura da kafafen yada labarai ta Nijeriya NBC tace tarar kafar yada labari ta Channels TV bisa wata tattaunawa da tayi da wanda ya yi wa Jam’iyyar LP takarar mataimakin shugaban kasa a kakar zaben shekarar 2023 Baba-Ahmed.

Ta cikin Shirin Politics Today na makon daya gabata Baba-Ahmed ya bukaci babban Alkalin alkalan Nijeriya Olukayode Ariwoola da kada ya rantsar da Bola tinubu matsayin shugaban kasa.

Dan takarar mataimakin shugaban kasar na Jam’iyyar LP yace babu zababben shugaban kasa saboda Tinubu bai cika ka’idojin tsarin Mulki ba.

Kamfanin dillancin labaru na Nijeriya NAN ya rawaito cewa tarar na cikin wata sanarwa mai dauke da kwanan watan 27 mai dauke da adreshin baban daraktan tashar  na Channels.

shugaban hukumar ta NBC yace za ta iya tunzura jama’a tare da kawo hargitsi a ƙasar, don haka a cewar hukumar, ta saɓa wa dokokin yaɗa labarai.

lllelah ya ci gaba da cewa a lokuta da dama, hukumarsa ta sha faɗa wa gidan talabijin ɗin ya riƙa la’akari da zaman lafiyar ƙasar, kafin yaɗa kowanne irin shiri nasa.

Don haka ya ce hukumar ta sanya wa gidan talbijin ɗin tarar naira miliyan biyar a kan wannan saɓa ƙa’ida, tare da gargaɗin Channels TV ya kiyaye aukuwar irin hakan a nan gaba.

PRNigeria Hausa

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp