Home Labarai NBC ta ci tarar Tashar Channels Miliyan 5

NBC ta ci tarar Tashar Channels Miliyan 5

Hukumar dake lura da kafafen yada labarai ta Nijeriya NBC tace tarar kafar yada labari ta Channels TV bisa wata tattaunawa da tayi da wanda ya yi wa Jam’iyyar LP takarar mataimakin shugaban kasa a kakar zaben shekarar 2023 Baba-Ahmed.

Ta cikin Shirin Politics Today na makon daya gabata Baba-Ahmed ya bukaci babban Alkalin alkalan Nijeriya Olukayode Ariwoola da kada ya rantsar da Bola tinubu matsayin shugaban kasa.

Dan takarar mataimakin shugaban kasar na Jam’iyyar LP yace babu zababben shugaban kasa saboda Tinubu bai cika ka’idojin tsarin Mulki ba.

Kamfanin dillancin labaru na Nijeriya NAN ya rawaito cewa tarar na cikin wata sanarwa mai dauke da kwanan watan 27 mai dauke da adreshin baban daraktan tashar  na Channels.

shugaban hukumar ta NBC yace za ta iya tunzura jama’a tare da kawo hargitsi a ƙasar, don haka a cewar hukumar, ta saɓa wa dokokin yaɗa labarai.

lllelah ya ci gaba da cewa a lokuta da dama, hukumarsa ta sha faɗa wa gidan talabijin ɗin ya riƙa la’akari da zaman lafiyar ƙasar, kafin yaɗa kowanne irin shiri nasa.

Don haka ya ce hukumar ta sanya wa gidan talbijin ɗin tarar naira miliyan biyar a kan wannan saɓa ƙa’ida, tare da gargaɗin Channels TV ya kiyaye aukuwar irin hakan a nan gaba.

PRNigeria Hausa

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp