Home Labarai NBC ta ci tarar Tashar Channels Miliyan 5

NBC ta ci tarar Tashar Channels Miliyan 5

Hukumar dake lura da kafafen yada labarai ta Nijeriya NBC tace tarar kafar yada labari ta Channels TV bisa wata tattaunawa da tayi da wanda ya yi wa Jam’iyyar LP takarar mataimakin shugaban kasa a kakar zaben shekarar 2023 Baba-Ahmed.

Ta cikin Shirin Politics Today na makon daya gabata Baba-Ahmed ya bukaci babban Alkalin alkalan Nijeriya Olukayode Ariwoola da kada ya rantsar da Bola tinubu matsayin shugaban kasa.

Dan takarar mataimakin shugaban kasar na Jam’iyyar LP yace babu zababben shugaban kasa saboda Tinubu bai cika ka’idojin tsarin Mulki ba.

Kamfanin dillancin labaru na Nijeriya NAN ya rawaito cewa tarar na cikin wata sanarwa mai dauke da kwanan watan 27 mai dauke da adreshin baban daraktan tashar  na Channels.

shugaban hukumar ta NBC yace za ta iya tunzura jama’a tare da kawo hargitsi a ƙasar, don haka a cewar hukumar, ta saɓa wa dokokin yaɗa labarai.

lllelah ya ci gaba da cewa a lokuta da dama, hukumarsa ta sha faɗa wa gidan talabijin ɗin ya riƙa la’akari da zaman lafiyar ƙasar, kafin yaɗa kowanne irin shiri nasa.

Don haka ya ce hukumar ta sanya wa gidan talbijin ɗin tarar naira miliyan biyar a kan wannan saɓa ƙa’ida, tare da gargaɗin Channels TV ya kiyaye aukuwar irin hakan a nan gaba.

PRNigeria Hausa

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp