Home Labarai Sojojin Nijeriya sun hallaka ‘yan bindiga 5 tare da kwato makamai a...

Sojojin Nijeriya sun hallaka ‘yan bindiga 5 tare da kwato makamai a jihar Kaduna

Dakarun sojojin Nijeriya runduna ta daya dake aiki a karamar hukumar Chikum a jihar kaduna, sun sami nasarar fatattakar ‘yan bindiga biyar tare da kwato bindigu kirar Ak-7 guda 6 da kuma gidan Alburusai na bindigar AK47 guda shida da kuma wani Alburushi masu tsayin 7.62mm guda 24.

Wannan na kunshe ta cikin wata sanarwa mai dauke da sa hannun mukaddashin mai Magana da yawun rundunar shiyya ta  daya Lt-Col Musa Yahaya ya fitar a jihar Kaduna.

Yahaya ya bayyana cewa dakarun sun gudanar da atisayen a yankin kan tudun Kaso da kanti zuwa Tantatu a dajin Kubusu dake jihar.

Yace atisayen ya kasance wani bangare na dakile ayyukan ‘yan fashi da masu aikata laifuka domin inganat tsaro da dawo da tattalin arziki mai dorewa a ‘yankin.”

Yahaya ya kara da cewa an fara atisayen ne a tsakar dare juma’a wanda ya sanya ‘yan bindigar suka jigata matuka.

Inda y ace sun sami nasarar kwato Babura hawa guda 3, wayar salula guda biyu da sauran kayayyakin amfani.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp