Home Labarai Sojojin Nijeriya sun hallaka ‘yan bindiga 5 tare da kwato makamai a...

Sojojin Nijeriya sun hallaka ‘yan bindiga 5 tare da kwato makamai a jihar Kaduna

Dakarun sojojin Nijeriya runduna ta daya dake aiki a karamar hukumar Chikum a jihar kaduna, sun sami nasarar fatattakar ‘yan bindiga biyar tare da kwato bindigu kirar Ak-7 guda 6 da kuma gidan Alburusai na bindigar AK47 guda shida da kuma wani Alburushi masu tsayin 7.62mm guda 24.

Wannan na kunshe ta cikin wata sanarwa mai dauke da sa hannun mukaddashin mai Magana da yawun rundunar shiyya ta  daya Lt-Col Musa Yahaya ya fitar a jihar Kaduna.

Yahaya ya bayyana cewa dakarun sun gudanar da atisayen a yankin kan tudun Kaso da kanti zuwa Tantatu a dajin Kubusu dake jihar.

Yace atisayen ya kasance wani bangare na dakile ayyukan ‘yan fashi da masu aikata laifuka domin inganat tsaro da dawo da tattalin arziki mai dorewa a ‘yankin.”

Yahaya ya kara da cewa an fara atisayen ne a tsakar dare juma’a wanda ya sanya ‘yan bindigar suka jigata matuka.

Inda y ace sun sami nasarar kwato Babura hawa guda 3, wayar salula guda biyu da sauran kayayyakin amfani.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp