Home DUNIYA Akwai yiwuwar kotun ICC ta yi amfani da Afrika ta kudu wajen...

Akwai yiwuwar kotun ICC ta yi amfani da Afrika ta kudu wajen kame Putin

Hankulan duniya sun karkata kan Afrika ta Kudu kasar da ake ganin kotun Duniya ta ICC na shirin amfani da ita wajen kame shugaba Vladimir Putin na Rasha wanda kotun ta fitar da takardar sammacin kamen shi a ranar 17 ga watan Maris din da muka yi bakwana da shi.

Alamomi na nuni da cewa ita kanta gwamnatin shugaba Cyril Ramaphosa na halin tsaka mai wuya lura da yadda jagoran na Moscow ke Shirin ziyartar kasar a watan Agusta mai zuwa don halartar taron kungiyar BRICS.

Karkashin dokokin kotun hukuntan manyan laifukan ta ICC wadda Afrika ta kudu ke matsayin mamba a cikinta, wajibi ne kasar ta mika duk wani da kotun ke nema da zarar ya sanya kafa a Pretoria, lamarin da ke matsayin babbar damuwa ga ziyarar ta Putin.

Tun zamanin mulkin Nelson Mandela a shekarun 1988 Afrika ta kudu ke karkashin kotun ta Duniya tare da mutunta hukunce-hukuncenta, sai dai ana ganin abu ne mai wuya kasar ta amince da zama sanadin mika Putin lura da alakar Rasha da kasar.

Ministan da ke kula da alakar kasar da ketare, Naledi Pandor ya shaidawa manema labarai cewa yanzu haka suna tattaunawa don samun haske kan yadda za su tunkari wannan matsala.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp