Home DUNIYA Akwai yiwuwar kotun ICC ta yi amfani da Afrika ta kudu wajen...

Akwai yiwuwar kotun ICC ta yi amfani da Afrika ta kudu wajen kame Putin

Hankulan duniya sun karkata kan Afrika ta Kudu kasar da ake ganin kotun Duniya ta ICC na shirin amfani da ita wajen kame shugaba Vladimir Putin na Rasha wanda kotun ta fitar da takardar sammacin kamen shi a ranar 17 ga watan Maris din da muka yi bakwana da shi.

Alamomi na nuni da cewa ita kanta gwamnatin shugaba Cyril Ramaphosa na halin tsaka mai wuya lura da yadda jagoran na Moscow ke Shirin ziyartar kasar a watan Agusta mai zuwa don halartar taron kungiyar BRICS.

Karkashin dokokin kotun hukuntan manyan laifukan ta ICC wadda Afrika ta kudu ke matsayin mamba a cikinta, wajibi ne kasar ta mika duk wani da kotun ke nema da zarar ya sanya kafa a Pretoria, lamarin da ke matsayin babbar damuwa ga ziyarar ta Putin.

Tun zamanin mulkin Nelson Mandela a shekarun 1988 Afrika ta kudu ke karkashin kotun ta Duniya tare da mutunta hukunce-hukuncenta, sai dai ana ganin abu ne mai wuya kasar ta amince da zama sanadin mika Putin lura da alakar Rasha da kasar.

Ministan da ke kula da alakar kasar da ketare, Naledi Pandor ya shaidawa manema labarai cewa yanzu haka suna tattaunawa don samun haske kan yadda za su tunkari wannan matsala.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
https://nnn.ng/image-compressor/
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp