Home DUNIYA Akwai yiwuwar kotun ICC ta yi amfani da Afrika ta kudu wajen...

Akwai yiwuwar kotun ICC ta yi amfani da Afrika ta kudu wajen kame Putin

Hankulan duniya sun karkata kan Afrika ta Kudu kasar da ake ganin kotun Duniya ta ICC na shirin amfani da ita wajen kame shugaba Vladimir Putin na Rasha wanda kotun ta fitar da takardar sammacin kamen shi a ranar 17 ga watan Maris din da muka yi bakwana da shi.

Alamomi na nuni da cewa ita kanta gwamnatin shugaba Cyril Ramaphosa na halin tsaka mai wuya lura da yadda jagoran na Moscow ke Shirin ziyartar kasar a watan Agusta mai zuwa don halartar taron kungiyar BRICS.

Karkashin dokokin kotun hukuntan manyan laifukan ta ICC wadda Afrika ta kudu ke matsayin mamba a cikinta, wajibi ne kasar ta mika duk wani da kotun ke nema da zarar ya sanya kafa a Pretoria, lamarin da ke matsayin babbar damuwa ga ziyarar ta Putin.

Tun zamanin mulkin Nelson Mandela a shekarun 1988 Afrika ta kudu ke karkashin kotun ta Duniya tare da mutunta hukunce-hukuncenta, sai dai ana ganin abu ne mai wuya kasar ta amince da zama sanadin mika Putin lura da alakar Rasha da kasar.

Ministan da ke kula da alakar kasar da ketare, Naledi Pandor ya shaidawa manema labarai cewa yanzu haka suna tattaunawa don samun haske kan yadda za su tunkari wannan matsala.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp