Home SIYASA Ku dakata da bai wa gwamnatin Kano bashi- Abba Gida-gida

Ku dakata da bai wa gwamnatin Kano bashi- Abba Gida-gida

Sabon zaɓaɓɓen gwamnan jihar Kano Engr. Abba Kabir Yusuf ya shawarci masu bai wa gwamnatin jihar bashi da cewa su dakata.

wannan na kunshe ta cikin wata sanarwa da sakataren yaɗa labaran sabon zaɓaɓɓen gwamnan Sunusi Bature Dawaki Tofa ya fitar, inda tace sabon gwamnan ya shawarci masu bai wa gwamnatin jihar bashi na cikin gida da na waje da kada su amince da bai wa gwamnatin jihar bashi daga ranar 18 ga watan Maris zuwa ranar 29 ga watan Mayu.

Sanarwar ta ci gaba da cewa sabuwar gwamnatin ba za ta yi la’akari da bashin da jihar ta karɓa, ba tare da saninta ba daga ranar zaɓe zuwa ranar da aka rantsar da sabuwar gwamnatin.

Haka kuma sanarwar ta ce masu bin gwamnatin jihar bashi a yanzu su kwana da sanin cewa za a sake nazarin ƙa’idojin bashin bayan kammala bincike a kan kowanne bashi da ake bin jihar.

Ko a makon da ya gabata ma sabon zaɓaɓɓen gwamnan ya bayar da shawara ga masu gine-gine a filayen gwamantin jihar da su dakatar da ayyukansu.

To sai dai ‘yan kwanaki bayan shawarar zaɓaɓɓen gwamnan, gwamnan jihar mai barin gado Abdullahi Umar Ganduje ya mayar masa da martani, yana mai cewa sabon gwamnan ya yi haƙuri, ya daina fitar da sanarwar hukuma da sunan shawara ga jama’a.

duk da cewa ana kallon martanin na Gandujen ka iya zama musayar yawu tsakanin Gwamnatin mai ci da mai barin gado.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp