Home Labarai ‘Yan bindiga sun sace dalibai mata biyu na jami’ar Gusau

‘Yan bindiga sun sace dalibai mata biyu na jami’ar Gusau

‘Yan bindiga sun sace ɗalibai mata guda biyu a jami’ar tarayya da ke Gusau a jihar Zamfara, arewa maso yammacin Najeriya.

Rahotonni sun ce ‘yan fashin ɗauke da muggan makamai, sun sace ɗaliban ne a ɗakunan kwanansu da ke wajen makarantar.

Wata sanarwa da rundunar ‘yan sandan jihar ta fitar, ta ambato kwamishinan ‘yan sandan Zamfara, CP Kolo Yusuf na tabbatar wa iyayen ɗaliban da kuma hukumar makarantar cewa rundunar tana ƙoƙari don ganin ta kuɓutar da su.

Ta ce ‘yan sanda sun samu rahoton sace ɗaliban a ɗakunan kwanansu da ke a wajen makarantar, kuma ba ta yi ƙasa a gwiwa ba, ta tura jami’anta zuwa wajen da lamarin ya auku.

Sai dai kafin zuwan jami’an tsaron ‘yan fashin sun tsere da ɗaliban, kamar yadda sanarwar ta bayyana.

Haka kuma sanarwar ta ce kwamishinan ‘yan sandan ya tura ƙarin jami’an tsaro don bin sawun ‘yan fashin da kuma kuɓutar da ɗaliban.

Zamfara, ta yi ƙaurin suna a matsayin jihar da ‘yan fashin daji suka mamaye wasu sassanta, inda suke kai hare-hare da sace mutane a ciki har wajen jihar suna neman kuɗin fansa daga makusanta da dangin waɗanda abin ya ritsa da su.

An yi imani har yanzu akwai ragowar daliban kwalejin tarayya ta Yawuri kimanin 11 dukkansu mata, waɗanda aka sato daga jihar Kebbi mai maƙwabtaka, kuma ake ci gaba da tsarewa a wani daji da ke cikin Zamfara wanda a yanzu sun kwashe kwanan 653.

Ranar 16 ga watan Yunin 2021 ne, ‘yan bindigar suka sace ɗaliban su kimanin 100 tare da wasu malamansu, inda suka tafi da su daji, kafin daga bisani su saki mafi yawansu cikin rukuni-rukuni.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp