Gwamnati ta shirya muƙabala da Sheikh Idris game da kalamansa a kan Annabi

Hukumar Shari’a ta Jihar Bauchi a Arewa mask gabashin Najeriya ta shirya muƙabala tsakanin malamai da kuma Sheikh Idris Abdul’aziz Dutsen Tanshi kan kalaman da ya yi game da Annabi Muhammadu (SAW).

Wata wasiƙa da hukumar ta aike wa malamin, ɗan asalin jihar Bauchi, ta ce za a gudanar da tattaunawar ilimin ne gobe Asabar, 8 ga watan Afrilu a birnin Bauchi.

A farkon makon nan ne kalaman malamin suka fara tayar da hazo musamman a shafukan zumunta, bayan ya yi iƙirarin cewa “ba ya buƙatar taimakon Annabi”.

“Ana gayyatar ka zuwa tattaunawa ta ilimi [munaƙasha] game da kalamanka cewa ‘kai! …Manzon Allah ma ba ma son taimakonsa, ƙarewarta kenan’,” kamar yadda hukumar ta bayyana cikin wasiƙar.

An ga malamin ya bayyana cikin wani bidiyo a ranar Alhamis yana cewa ya ji daga wata majiya cewa zai yi muhawara da wakilan wasu ƙungiyoyin addini a jihar, waɗanda suka haɗa da Izala da ɗariƙa.

An yi irin wannan muhawara a Kano cikin watan Yulin 2021 lokacin da aka zargi Sheikh Abduljabbar Nasiru Kabara da yin kalaman ɓatanci ga Annabin Muhammadu.

Bayan muhawarar ne kuma, hukumomi suka gurfanar da malamin a gaban kotu, wadda ta yanke masa hukuncin kisa.

PRNigeria Hausa

 

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1190 days 9 hours 14 minutes 12 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1172 days 10 hours 55 minutes 37 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com