Home Labarai Babban aikin da ke gaban Musulman duniya shine yada Addini na gaskiya...

Babban aikin da ke gaban Musulman duniya shine yada Addini na gaskiya – Buhari

Shugaban Nijeriya Muhammadu Buhari ya ce babban aiki mafi muhimmanci da ke gaban Musulman duniya a yau shi ne yada akidu da ilimin addinin Musulunci na gaskiya.

Shugaba Buhari ya bayyana hakan ne a birnin Madina na kasar Saudiyya, a ziyarar aikin Umara da yake yi.

A cikin wata sanarwa da aka fitar mai dauke da sa hannun Malam Garba Shehu, mai bai wa shugaban shawara kan kafafen yada labarai, Buhari ya kuma yaba wa gwamnatin Saudiyyar bisa yadda ta samar da kayayyakin zamani wajen yada Musulunci da sanin manufarsa a ilmance kuma ta hanya mafi inganci.

Da yake bayani bayan rangadi a wajen baje-kolin kasa da kasa da kuma zagaya gidan adana kayan tarihin fiyayyen halitta Annabi Muhammad SWA da Sakafar Musulunci a wani bangare na ayyukan da yake yi a Saudiyya, Shugaban Nijeriyar ya ce al’ummar Musulmai na bukatar tsari ingantacce da zai bayar da hikima da ilimi domin kyakkyawar fahimtar addinin.

Buhari Ya yaba wa mahukuntan Saudiyya bisa yadda suka yi kokarin yada sakafar Musulunci a duniya, amma kuma ana bukatar karin ayyuka da dama.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp