Home SIYASA zaben 2023: APC ta Maka Abba gida-gida gaban Kotu

zaben 2023: APC ta Maka Abba gida-gida gaban Kotu

Jam’iyyar APC reshen jihar Kano da ke Najeriya ta shigar da kara a gaban kotun sauraren korafe-korafen zaben gwamna, inda take kalubalantar Hukumar Zaben Kasar ta INEC kan yadda ta ayyana Abba Kabir Yusuf na jam’iyyar NNPP a matsayin wanda ya lashe zaben ranar 18 ga watan Maris.

Jam’iyyar ta APC ta ce, Yusuf, wanda aka fi sani da Abba Gida-Gida bai cancanci tsayawa takara a zaben ba saboda a cewarta, sunansa ba ya cikin jerin sunayen mambobin jam’iyyar NNPP ta aika wa INEC.

Kazalika APC ta yi zargin cewa, NNPP ba ta lashe zaben ba musamman ganin yadda aka kidaya wa jam’iyyar hatta kuri’un da suka lalace a cewarta, kuma tana ganin cewa, da an cire lalatattun kuri’un, da ita za ta yi nasara.

Koda yake, dan takarar gwamnan na jam’iyyar APC, Nasiru Yusuf Gawuna bai yi tarayya da jam’iyyar ba wajen shigar da wannan koken.

Tuni dai Gawuna ya amince da shan kayi a zaben wanda sakamakonsa ya nuna cewa, Abba Gida-Gida ya samu kuri’u miliyan 1 da dubu 19  da 602, yayin da shi kuma ya samu kuri’u dubu 890 da 705.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp