Home DUNIYA IMF ta ayyana Nijeriya a sahun kasashe na gaba-gaba wajen samun bunkasar...

IMF ta ayyana Nijeriya a sahun kasashe na gaba-gaba wajen samun bunkasar tattalin arziki.

Asusun Lamuni na Duniya, wato IMF ya fitar da sabon rahoto na ‘Hasashen Tattalin Arzikin’ kasashen duniya na shekarar 2023 da na 2024.

A cikinsa, IMF ta ayyana Nijeriya a sahun kasashe na gaba-gaba a samun bunkasar tattalin arziki, da karin kashi 3.2% a ma’aunin GDP.

Nijeriya tana rukunin sabbin kasuwanni ko masu tattalin arzikin mai tasowa, inda take ta uku, da kashi 3.2%, sai ta biyu, China da kashi 5.2%, sai kuma Indiya da ta kasance ta daya, da kashi 5.9.

Idan aka duba cikin kasashen da ke Kudu da Sahara, yankin da ake yi wa kallon yana cikin mafi karancin ci gaba, Nijeriya ta doke Afirka ta Kudu wadda ke da kashi 0.1% kacal a 2023.

Pierre-Olivier Gourinchas, shi ne babban jami’in tattalin arzikin na IMF, yayin gabatar da rahoton, ya bayyana cewa tattalin arzikin duniya yana farfadowa duk kuwa da kangin da bankuna suka shiga a baya-bayan nan.

Sabon rahoton ya fitar da wani jadawali na jerin sauye-sauyen farashin kayayyakin amfanin jama’a, da za a samu a wannan shekara a kasashen duniya.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp