Home DUNIYA IMF ta ayyana Nijeriya a sahun kasashe na gaba-gaba wajen samun bunkasar...

IMF ta ayyana Nijeriya a sahun kasashe na gaba-gaba wajen samun bunkasar tattalin arziki.

IMF

Asusun Lamuni na Duniya, wato IMF ya fitar da sabon rahoto na ‘Hasashen Tattalin Arzikin’ kasashen duniya na shekarar 2023 da na 2024.

A cikinsa, IMF ta ayyana Nijeriya a sahun kasashe na gaba-gaba a samun bunkasar tattalin arziki, da karin kashi 3.2% a ma’aunin GDP.

Nijeriya tana rukunin sabbin kasuwanni ko masu tattalin arzikin mai tasowa, inda take ta uku, da kashi 3.2%, sai ta biyu, China da kashi 5.2%, sai kuma Indiya da ta kasance ta daya, da kashi 5.9.

Idan aka duba cikin kasashen da ke Kudu da Sahara, yankin da ake yi wa kallon yana cikin mafi karancin ci gaba, Nijeriya ta doke Afirka ta Kudu wadda ke da kashi 0.1% kacal a 2023.

Pierre-Olivier Gourinchas, shi ne babban jami’in tattalin arzikin na IMF, yayin gabatar da rahoton, ya bayyana cewa tattalin arzikin duniya yana farfadowa duk kuwa da kangin da bankuna suka shiga a baya-bayan nan.

Sabon rahoton ya fitar da wani jadawali na jerin sauye-sauyen farashin kayayyakin amfanin jama’a, da za a samu a wannan shekara a kasashen duniya.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp