Home Labarai Gwamnatin Najeriya za ta kashe naira biliyan 250 don rage talauci bana

Gwamnatin Najeriya za ta kashe naira biliyan 250 don rage talauci bana

Gwamnatin Najeriya ta amince a kashe naira biliyan 250 a bana, a shirinta na rage talauci da take gudanarwa a faɗin ƙasar.

Mataimakin shugaban Najeriya, Yemi Osinbajo ne ya bayyana hakan yayin wani jawabi da ya yi kan rahoton ci gaban da aka samu a shirin rage talaucin na ƙasa da ake kira NPRGS a gaban kwamitin da ya jagoranta ranar Laraba.

Ayyukan da aka tsara aiwatarwa a 2023 ƙarƙashin shirin NPRGS sun haɗa da: “Gina gidaje dubu ɗari ga masu ƙaramin ƙarfi, aikin da zai samar da ayyukan yi miliyan ɗaya na kai-tsaye ko a kaikaice.

“Faɗaɗa samun makamashi ta hanyar samar da fitilun gefen titi 1,200 a yankunan karkara da kuma wasu ƙananan tashoshin lantarki da za a riƙa amfani da su a gonaki ƙarƙashin wani shiri mai suna Solar Naija.

“Samar da ayyuka miliyan huɗu da ɗari biyar na kai-tsaye ko kuma a kaikaice ta hanyar shirin gina hanyoyi a yankin karkara da za su haɗa kasuwannin ƙauye 750 a faɗin Najeriya.

“Samar da tallafin naira biliyan tara ga manoma masu ƙaramin ƙarfi a daminar bana karkashin shirin samar da aikin yi a bangaren noma.

“Fadada rijistar mutanen da ke samun tallafin rayuwa da ƙarin magidanta miliyan uku.”

A lokacin gabatar da bayanin, ministan kasafin kudi da tsare tsare, Clem Agba, ya ce mutum miliyan biyu ne suka amfana da shirin NPRGS kai-tsaye a 2022.

Rahotonsa ya bayyana cewa manoma miliyan daya da dubu 600 ne suka amfana da shirin a karkashin shirin habbaka noma.

Wata sanarwa da mai magana da yawun mataimakin shugaban Najeriyan ya fitar a jiya, ta ce matasa 13,000 ne suka samu horo kan ƙere-ƙere da kuma sana’o’in hannu a jihohi 6 da suka hada da Legas da Ogun da Enugu da Gombe da Kaduna da kuma Nasarawa, yayin da ake shirin samar da irin wannan tsari ga matasa 2,000 a jihar Edo.

Ya ce ‘yan Najeriya fiye da 8,000 aka ɗauka aikin shimfiɗa tituna a yankunan karkara ƙarƙashin shirin samar da hanyoyi a karkara, inda aka gina hanya 40 da suka ratsa kauyuka 120 a faɗin Najeriya.

“A duk faɗin Najeriya mutum 1,818,782 ne suke cin gajiyar shirin NPRGS, kuma an ɗauki mutum 9,527 aiki ƙarƙashin aikin ya zuwa yanzu.”

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp