Home DUNIYA Fada ya kaure tsakanin sojojin Sudan da runduna ta musamman

Fada ya kaure tsakanin sojojin Sudan da runduna ta musamman

An ji karar fashe fashe a babban birnin Sudan, Khartoum a yau Asabar, sakamakon rikicin da ya kaure tsakanin dakaru na musamman da ke gadin fadar shugaban kasar da sojoji, kwanaki bayan da rundunar sojin kasar ta yi kashedin cewa kasar ta shiga wani matsayi mai hatsari.

Rikicin ya  barke ne  bayan da aka shafe makwanni ana zaman tankiya tsakanin jagoran gwamnatin sojin kasar, Janar Abdel Fattah al-Burhan da mataimakinsa, kuma kwamandan runduna ta musamman na kasar, Hamdan Daglo.

Ganau sun ruwaito cewa an yi arangama, inda aka ji karar fashe fashe a kusa da ofishin runduna ta musamman, wato RSF.

Runduna ta musamman ta ce dakarunta sun karbe iko da filin jirgin sama na birnin Khartoum a halin da ake ciki, bayan da shaidu suka ce sun hango motoci cike da mayaka na shiga cikin harabar filin jirgin saman.

sun ruwaito cewa sun jiyo karar  harbe harbe a kusa da filin jirgin saman, da kuma kusa da gidan Burhan a arewacin birnin Khartoum.

An hango fararen hula suna ta tserewa don tsira da rayukansu.

Bangarorin biyu dai na zargin jina da  tada rikicin.

Jagoran mulkin sojin Sudan, Burhan da mataimakainsa suna cikin rashin jituwa ne a kan tattaunawar yarjejeniyar mika mulki ga farar hula tare da karshen rikicin da ya kunno kai tun bayan juyin mulkin shekarar 2021.

Runduna ta musamman ta RSF da aka kirkiro  a shekarar 2013 ta sao asali ne daga kungiyaar ‘yaan tsagerar Janjaweed, wadda tsohon shugaban kasar, Omar al-Bashir ya yi amafani da ita wajen muzgunawa ‘yan tsirarun kabilu wadanda ba Larabawa ba a yankin yammacin Darfur, lamarin da yanzu ya janyo masa tuhumar aikata laifukan yaki.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp