Home DUNIYA Tarayyar Afirka ta yi kira a dakatar da abin da ta kira...

Tarayyar Afirka ta yi kira a dakatar da abin da ta kira ‘ruguza Sudan’

Shugaban Hukumar Tarayyar Afirka, Moussa Faki Mahamat, ya fitar da wata sanarwa kan abin da ke ci gaba da faruwa a Sudan.

Sanarwar ta ambato shugaban Tarayyar Afirka na roƙon “ɓangarorin siyasa da soji su samo mafitar siyasa ta adalci ga rikicin da ya taso bayan juyin mulkin 25 ga watan Oktoban 2021 da kuma miyagun abubuwan da suka biyo baya.

Mahamat na magana ne kan abin da ke faruwa game da ranar da sojojin Sudan ƙarƙashin jagorancin Janar Abdel Fattah al-Burhan suka ƙwace iko da gwamnati a Sudan.

Sanarwar Mista Mahamat ta yi kira ga sojoji da kuma dakarun RSF masu kayan sarki cewa: “Cikin gaggawa a dakatar da ruguza ƙasar, da tafka ta’addanci ga al’ummarta, da kuma zubar da jini a wannan lokaci na goman ƙarshe cikin watan Ramadan mai alfarma”.

An dakatar da Sudan daga ƙungiyar ƙasashen ta Tarayyar Afirka a watan Yunin 2019.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp