Home DUNIYA Tarayyar Afirka ta yi kira a dakatar da abin da ta kira...

Tarayyar Afirka ta yi kira a dakatar da abin da ta kira ‘ruguza Sudan’

Shugaban Hukumar Tarayyar Afirka, Moussa Faki Mahamat, ya fitar da wata sanarwa kan abin da ke ci gaba da faruwa a Sudan.

Sanarwar ta ambato shugaban Tarayyar Afirka na roƙon “ɓangarorin siyasa da soji su samo mafitar siyasa ta adalci ga rikicin da ya taso bayan juyin mulkin 25 ga watan Oktoban 2021 da kuma miyagun abubuwan da suka biyo baya.

Mahamat na magana ne kan abin da ke faruwa game da ranar da sojojin Sudan ƙarƙashin jagorancin Janar Abdel Fattah al-Burhan suka ƙwace iko da gwamnati a Sudan.

Sanarwar Mista Mahamat ta yi kira ga sojoji da kuma dakarun RSF masu kayan sarki cewa: “Cikin gaggawa a dakatar da ruguza ƙasar, da tafka ta’addanci ga al’ummarta, da kuma zubar da jini a wannan lokaci na goman ƙarshe cikin watan Ramadan mai alfarma”.

An dakatar da Sudan daga ƙungiyar ƙasashen ta Tarayyar Afirka a watan Yunin 2019.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp