Home DUNIYA Tarayyar Afirka ta yi kira a dakatar da abin da ta kira...

Tarayyar Afirka ta yi kira a dakatar da abin da ta kira ‘ruguza Sudan’

Shugaban Hukumar Tarayyar Afirka, Moussa Faki Mahamat, ya fitar da wata sanarwa kan abin da ke ci gaba da faruwa a Sudan.

Sanarwar ta ambato shugaban Tarayyar Afirka na roƙon “ɓangarorin siyasa da soji su samo mafitar siyasa ta adalci ga rikicin da ya taso bayan juyin mulkin 25 ga watan Oktoban 2021 da kuma miyagun abubuwan da suka biyo baya.

Mahamat na magana ne kan abin da ke faruwa game da ranar da sojojin Sudan ƙarƙashin jagorancin Janar Abdel Fattah al-Burhan suka ƙwace iko da gwamnati a Sudan.

Sanarwar Mista Mahamat ta yi kira ga sojoji da kuma dakarun RSF masu kayan sarki cewa: “Cikin gaggawa a dakatar da ruguza ƙasar, da tafka ta’addanci ga al’ummarta, da kuma zubar da jini a wannan lokaci na goman ƙarshe cikin watan Ramadan mai alfarma”.

An dakatar da Sudan daga ƙungiyar ƙasashen ta Tarayyar Afirka a watan Yunin 2019.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp