Home Labarai Babban aikin da ke gaban Musulman duniya shine yada Addini na gaskiya...

Babban aikin da ke gaban Musulman duniya shine yada Addini na gaskiya – Buhari

Shugaban Nijeriya Muhammadu Buhari ya ce babban aiki mafi muhimmanci da ke gaban Musulman duniya a yau shi ne yada akidu da ilimin addinin Musulunci na gaskiya.

Shugaba Buhari ya bayyana hakan ne a birnin Madina na kasar Saudiyya, a ziyarar aikin Umara da yake yi.

A cikin wata sanarwa da aka fitar mai dauke da sa hannun Malam Garba Shehu, mai bai wa shugaban shawara kan kafafen yada labarai, Buhari ya kuma yaba wa gwamnatin Saudiyyar bisa yadda ta samar da kayayyakin zamani wajen yada Musulunci da sanin manufarsa a ilmance kuma ta hanya mafi inganci.

Da yake bayani bayan rangadi a wajen baje-kolin kasa da kasa da kuma zagaya gidan adana kayan tarihin fiyayyen halitta Annabi Muhammad SWA da Sakafar Musulunci a wani bangare na ayyukan da yake yi a Saudiyya, Shugaban Nijeriyar ya ce al’ummar Musulmai na bukatar tsari ingantacce da zai bayar da hikima da ilimi domin kyakkyawar fahimtar addinin.

Buhari Ya yaba wa mahukuntan Saudiyya bisa yadda suka yi kokarin yada sakafar Musulunci a duniya, amma kuma ana bukatar karin ayyuka da dama.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp