Home Labarai Babban aikin da ke gaban Musulman duniya shine yada Addini na gaskiya...

Babban aikin da ke gaban Musulman duniya shine yada Addini na gaskiya – Buhari

Shugaban Nijeriya Muhammadu Buhari ya ce babban aiki mafi muhimmanci da ke gaban Musulman duniya a yau shi ne yada akidu da ilimin addinin Musulunci na gaskiya.

Shugaba Buhari ya bayyana hakan ne a birnin Madina na kasar Saudiyya, a ziyarar aikin Umara da yake yi.

A cikin wata sanarwa da aka fitar mai dauke da sa hannun Malam Garba Shehu, mai bai wa shugaban shawara kan kafafen yada labarai, Buhari ya kuma yaba wa gwamnatin Saudiyyar bisa yadda ta samar da kayayyakin zamani wajen yada Musulunci da sanin manufarsa a ilmance kuma ta hanya mafi inganci.

Da yake bayani bayan rangadi a wajen baje-kolin kasa da kasa da kuma zagaya gidan adana kayan tarihin fiyayyen halitta Annabi Muhammad SWA da Sakafar Musulunci a wani bangare na ayyukan da yake yi a Saudiyya, Shugaban Nijeriyar ya ce al’ummar Musulmai na bukatar tsari ingantacce da zai bayar da hikima da ilimi domin kyakkyawar fahimtar addinin.

Buhari Ya yaba wa mahukuntan Saudiyya bisa yadda suka yi kokarin yada sakafar Musulunci a duniya, amma kuma ana bukatar karin ayyuka da dama.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp