Home Labarai Gwamnatin Najeriya za ta kashe naira biliyan 250 don rage talauci bana

Gwamnatin Najeriya za ta kashe naira biliyan 250 don rage talauci bana

Gwamnatin Najeriya ta amince a kashe naira biliyan 250 a bana, a shirinta na rage talauci da take gudanarwa a faɗin ƙasar.

Mataimakin shugaban Najeriya, Yemi Osinbajo ne ya bayyana hakan yayin wani jawabi da ya yi kan rahoton ci gaban da aka samu a shirin rage talaucin na ƙasa da ake kira NPRGS a gaban kwamitin da ya jagoranta ranar Laraba.

Ayyukan da aka tsara aiwatarwa a 2023 ƙarƙashin shirin NPRGS sun haɗa da: “Gina gidaje dubu ɗari ga masu ƙaramin ƙarfi, aikin da zai samar da ayyukan yi miliyan ɗaya na kai-tsaye ko a kaikaice.

“Faɗaɗa samun makamashi ta hanyar samar da fitilun gefen titi 1,200 a yankunan karkara da kuma wasu ƙananan tashoshin lantarki da za a riƙa amfani da su a gonaki ƙarƙashin wani shiri mai suna Solar Naija.

“Samar da ayyuka miliyan huɗu da ɗari biyar na kai-tsaye ko kuma a kaikaice ta hanyar shirin gina hanyoyi a yankin karkara da za su haɗa kasuwannin ƙauye 750 a faɗin Najeriya.

“Samar da tallafin naira biliyan tara ga manoma masu ƙaramin ƙarfi a daminar bana karkashin shirin samar da aikin yi a bangaren noma.

“Fadada rijistar mutanen da ke samun tallafin rayuwa da ƙarin magidanta miliyan uku.”

A lokacin gabatar da bayanin, ministan kasafin kudi da tsare tsare, Clem Agba, ya ce mutum miliyan biyu ne suka amfana da shirin NPRGS kai-tsaye a 2022.

Rahotonsa ya bayyana cewa manoma miliyan daya da dubu 600 ne suka amfana da shirin a karkashin shirin habbaka noma.

Wata sanarwa da mai magana da yawun mataimakin shugaban Najeriyan ya fitar a jiya, ta ce matasa 13,000 ne suka samu horo kan ƙere-ƙere da kuma sana’o’in hannu a jihohi 6 da suka hada da Legas da Ogun da Enugu da Gombe da Kaduna da kuma Nasarawa, yayin da ake shirin samar da irin wannan tsari ga matasa 2,000 a jihar Edo.

Ya ce ‘yan Najeriya fiye da 8,000 aka ɗauka aikin shimfiɗa tituna a yankunan karkara ƙarƙashin shirin samar da hanyoyi a karkara, inda aka gina hanya 40 da suka ratsa kauyuka 120 a faɗin Najeriya.

“A duk faɗin Najeriya mutum 1,818,782 ne suke cin gajiyar shirin NPRGS, kuma an ɗauki mutum 9,527 aiki ƙarƙashin aikin ya zuwa yanzu.”

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp