Home Labarai Rundunar ‘yan sandan jihar kano ta kama ‘yan daba jihar.

Rundunar ‘yan sandan jihar kano ta kama ‘yan daba jihar.

Rundunar ‘yan sandan jihar Kano da ke arewa maso yammacin Najeriya, ta kama wasu da ake zargi da aikata daba ta hanyar amfani da wuƙaƙe suna gallaza wa mutane a birnin Kano.

A cewar bayanai daga wajen waɗanda ayyukan ƴan dabar ya shafa, sun ce mutanen da ake tuhuma kan yi amfani da tituna masu cunkoso da wuraren taron jama’a don aikata ta’asar.

Duk da matsalar rashin tsaro, Kano cibiyar kasuwancin arewacin Najeriya, ta kasance cikin kwanciyar hankali har sai da aka samu gungun masu riƙe da wuƙaƙe.

Ayyukan ƴan dabar ya yi sanadiyyar mutuwar mutane bayan far musu da ɓata garin suka yi, yayin da waɗanda suka samu tsira kuma ke gamuwa da munanan raunuka.

’Yan dabar – waɗanda rundunar ‘yan sandan ta Anti-Daba ta kama – sun yi ƙaurin suna wajen amfani da wurare masu cunkoso don cin zarafin jama’a da rana tsaka.

Jami’in hulɗa da jama’a na ‘yan sandan, SP Abdullahi Haruna Kiyawa, ya yi kira ga jama’a da su taimaka rundunar wajen gano sauran ‘yan ƙungiyar dake cikin ƙwaryar birnin.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp