Home DUNIYA Janar-Janar da ke rikicin Sudan sun amince su tsagaita wuta ta tsohon...

Janar-Janar da ke rikicin Sudan sun amince su tsagaita wuta ta tsohon kanaki 3 – Blinken

Sakataren Harkokin Wajen Amurka Antony Blinken ya ce janar-janar da ke rikici a Sudan sun amince sun tsagaita wuta ta kwana uku ranar Litinin, bayan an kwashe kwana 10 ana fafatawa tsakaninsu.

Yarjejeniyoyin tsagaita wutar da suka kulla a baya ba su yi tasiri ba lamarin da ya kai ga kisan daruruwan mutane da kuma raba dubbai daga gidajensu.

Sai dai Blinken ya ce “bayan an kwashe sama da awa 48 ana tattaunawa sosai, Rundunar Sojin Sudan da Rapid Support Forces (RSF) sun amince su aiwatar da jarjejeniyar tsagaita wuta ta awa 72 daga ranar Litinin da daddare.”

Sakataren Wajen Amurka ya yi kalaman ne awa biyu kafin a soma aiwatar da yarjejeniyar.

Hakan na faruwa ne a lokacin da Babban Sakataren Majalisar Dinkin Duniya ya yi gargadin cewa Sudan na “dab da fadawa cikin bala’i” sakamakon rikici tsakanin bangarorin biyu, wadanda ke fafatawa a Khartoum da wasu bangarori na kasar.

An kashe akalla mutum 427 yayin da fiye da mutum 3,700 suka jikkata sakamakon rikicin, a cewar hukumomin Majalisar Dinkin Duniya.

Wani babban jami’in ofishin jakadancin Masar a Khartoum yana cikin wadanda aka kashe a baya bayan nan, a cewar ma’aikatar wajen kasar.

An kashe shi ne yayin da yake kan hanyar zuwa ofishin jakadancin domin sanin halin da ake ciki game da yiwuwar kwashe su daga Sudan.

Rikicin na faruwa ne tsakanin runsunar sojin da ke karkashin Janar Abdel Fattah al Burhan da dakarun RSF da ke karkashin tsohon mataimakinsa Janar Mohamed Hamdan Dagalo.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp