Home Labarai Rundunar ‘yan sandan jihar kano ta kama ‘yan daba jihar.

Rundunar ‘yan sandan jihar kano ta kama ‘yan daba jihar.

Rundunar ‘yan sandan jihar Kano da ke arewa maso yammacin Najeriya, ta kama wasu da ake zargi da aikata daba ta hanyar amfani da wuƙaƙe suna gallaza wa mutane a birnin Kano.

A cewar bayanai daga wajen waɗanda ayyukan ƴan dabar ya shafa, sun ce mutanen da ake tuhuma kan yi amfani da tituna masu cunkoso da wuraren taron jama’a don aikata ta’asar.

Duk da matsalar rashin tsaro, Kano cibiyar kasuwancin arewacin Najeriya, ta kasance cikin kwanciyar hankali har sai da aka samu gungun masu riƙe da wuƙaƙe.

Ayyukan ƴan dabar ya yi sanadiyyar mutuwar mutane bayan far musu da ɓata garin suka yi, yayin da waɗanda suka samu tsira kuma ke gamuwa da munanan raunuka.

’Yan dabar – waɗanda rundunar ‘yan sandan ta Anti-Daba ta kama – sun yi ƙaurin suna wajen amfani da wurare masu cunkoso don cin zarafin jama’a da rana tsaka.

Jami’in hulɗa da jama’a na ‘yan sandan, SP Abdullahi Haruna Kiyawa, ya yi kira ga jama’a da su taimaka rundunar wajen gano sauran ‘yan ƙungiyar dake cikin ƙwaryar birnin.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp