Home Labarai Rundunar ‘yan sandan jihar kano ta kama ‘yan daba jihar.

Rundunar ‘yan sandan jihar kano ta kama ‘yan daba jihar.

Rundunar ‘yan sandan jihar Kano da ke arewa maso yammacin Najeriya, ta kama wasu da ake zargi da aikata daba ta hanyar amfani da wuƙaƙe suna gallaza wa mutane a birnin Kano.

A cewar bayanai daga wajen waɗanda ayyukan ƴan dabar ya shafa, sun ce mutanen da ake tuhuma kan yi amfani da tituna masu cunkoso da wuraren taron jama’a don aikata ta’asar.

Duk da matsalar rashin tsaro, Kano cibiyar kasuwancin arewacin Najeriya, ta kasance cikin kwanciyar hankali har sai da aka samu gungun masu riƙe da wuƙaƙe.

Ayyukan ƴan dabar ya yi sanadiyyar mutuwar mutane bayan far musu da ɓata garin suka yi, yayin da waɗanda suka samu tsira kuma ke gamuwa da munanan raunuka.

’Yan dabar – waɗanda rundunar ‘yan sandan ta Anti-Daba ta kama – sun yi ƙaurin suna wajen amfani da wurare masu cunkoso don cin zarafin jama’a da rana tsaka.

Jami’in hulɗa da jama’a na ‘yan sandan, SP Abdullahi Haruna Kiyawa, ya yi kira ga jama’a da su taimaka rundunar wajen gano sauran ‘yan ƙungiyar dake cikin ƙwaryar birnin.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp