Home DUNIYA An wayi gari da karar harbe-harbe a Khartoum

An wayi gari da karar harbe-harbe a Khartoum

An shiga mako na biyu ana gwabza yaki a Sudan tsakanin sojojin kasar da kuma rundunar RSF, a daidai lokacin da wa’adin yarjejeniyar tsagaita wutar da aka cimmawa yazo karshe.

Harbe-harbe da karar fashewar bama-bamai sun lafa sai dai an wayi garin Asabar da karar harbe-harbe, wanda hakan alama ce ta rugujewar yarjejeniyar da aka cimmawa ta tsagaita wuta.

Duka bangarorin biyu dai sun ta ikirarin cewa za su tsagaita wuta sai dai abin ya ci tura.

Fiye da mutane 400 ne suka mutu yayin da dubbai suka jikkata tun bayan da fada ya kaure ranar Asabar tsakanin rundunar soji karkashin jagorancin babban hafsan soji Abdel Fattah da mataimakinsa, Mohamed Hamdan Daglo da aka fi sani Hemeti, wanda ke shugabantar rundunar (RSF).

Ranar Juma’a rundunar sojin ta sanar cewa ta “amince ta tsagaita wuta ta kwana uku” domin “bai wa ‘yan kasar damar yin bikin karamar Sallah da kuma bari a kai kayan agaji”, kamar yadda Babban Sakataren Majalisar Dinkin Duniya Antonio Guterres da Sakataren Wajen Amurka Antony Blinken suka bukaci a yi.

Ganau a yankuna da dama na Khartoum sun ce an kwashe tsawon Juma’a ba tare da jin karar harbe-harbe da luguden wuta ba.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp