Home DUNIYA Sama da Mutane dubu 3 sun rasa muhallin su a kasar Sudan

Sama da Mutane dubu 3 sun rasa muhallin su a kasar Sudan

Majalisar Dinkin Duniya ta ce mutane sama da 400 suka mutu ya zuwa wannan lokaci a rikicin kasar Sudan, yayin da sama da 3,500 suka samu raunuka daban daban.

Majlisar ta kuma kara da cewa daga cikin mutanen da suka mutu akwai yara kanana guda 9, bayan sama da 50 da suka jikkata.

Mai Magana da yawun hukumar lafiya ta duniya Margareth Harris ce ta gabatar da wadannan alkaluma masu tada hankali, sakamakon rahotannin da suke tattarawa daga hannun hukumomin lafiyar Sudan.

Harris ta ce yanzu haka asibitocin kula da lafiyar jama’a guda 20 sun daina aiki a Sudan saboda tashin hankalin, yayin da wasukarin 12 ke fuskantar barazanar dakatar da aikace aikacensu, wanda ake ganin na iya haifar da karin illa ga jama’a.

Shima mai Magana da yawun Hukumar da ke kula da kananan yara ta Majalisar wato UNICEF, James Elder ya ce rufe asibitocin ba wai kawai zai shafi wadanda suka samu raunuka sakamakon wannan tashin hankalin bane, har ma da marasa lafiyar da ke bukatar kulawa.

Elder ya ce dama kasar Sudan na daya daga cikin kasashen da ke da yawan yara masu fama da tamowa, kuma ganin yadda wannan rikici yayi kamari, ana iya samun karin yara kusan dubu 50 da za su fuskanci wannan matsala.

Rahotanni sun ce har a yau da juma’a ke bikin Sallar Idi, ana ta yin barín wuta tsakanin bangarorin biyu da ke kokawar mulki a cikin kasar.

Kungiyar likitoci ta kasa ta ce daren jiya anyi ta jin karar fashewar bama bamai da kuma amon makaman atilare a birnin Khartoum, yayin da sojojin gwamnati da na kungiyar RSF ke musayar wuta da bindigogi a tsakaninsu.

Sakatare Janar na Majalisar Dinkin Duniya Antonio Guterres tare da Sakataren harkokin wajen Amurka Antonio Blinken sun bukaci tsagaita wuta na tsawon kwanaki 3 domin bai wa jama’a damar gudanar da bukukuwan Sallah.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp