Home Labarai DSS ta kama ‘yan bindiga a Kano

DSS ta kama ‘yan bindiga a Kano

Hukumar Tsaro ta Farin Kaya a Nijeriya DSS ta ce ta kama wasu ‘yan bindiga biyu dauke da makamai a Jihar Kano da ke arewacin kasar.

wannan na unshe ta cikin wata sanarwa da rundunar ta fitar ranar Alhamis,  inda ta ce ta kama mutanen ne yayin da suke kan hanyarsu ta kai makaman wata jiha da zummar kaddamar da hare-hare.

Sanarwar, wadda kakakin DSS, Peter Afunanya ya sanya wa hannu ta kara da cewa an kwace makamai daban-daban daga hannun ‘yan bindigar.

Abubuwan da aka kama sun hada da bindiga kirar AK-47 guda biyu da kwanson harsasai na AK47 shi ma guda biyu da babur guda daya da kuma wani buhun doya da aka boye bindigogi.

“Hakan ya nuna cewa akwai bukatar mutane su lura da kyau sannan su kai rahoto ga jami’an tsaro da ke kusa da su kan duk wani motsi na mutanen da ba su amince da su ba,” a cewar Afunanya.

Hukumar tsaro ta yi kira ga wuraren shakatawa da su sanya ido sosai a lokacin bukukuwan karamar Sallah.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp