Rahotanni daga Nijeriya na bayyana cewa Mutane 214 ne suka mutu tsakanin watan Janairu da Maris din shekarar 2023, a hare-haren ‘yan bindiga da rikicin ƙabilanci da hare-haren ɗaukar fansa a jihar Kaduna a Najeriya.

A cikin wannan adadi 14 mata ne a yayin da huɗu yara ne ‘yan ƙasa da shekaru 18.

A gundumar Kaduna ta Tsakiya, an samu rahoton mutuwar mutane 115 (kashi 54 bisa dari na yawan adadin).

Ɗari da takwas na waɗannan adadi sun faru ne a yankunan ƙananan hukumomin Birnin Gwari, da Giwa, da Igabi, Chikun da kuma Kajuru.

Ƙananan hukumomi Giwa da Birnin Gwari duka sun samu yawan adadin mutane 32 da suka mutu, karamar hukumar Chikun 25, Igabi 13, sai Kajuru shida a watannin ukun farkon shekarar 2023.

A yankin kudancin Kaduna an samu mutuwar mutane 61 a daidai irin wannan lokaci.

Yanayin kai hare-hare da na daukar fansa, da munanan tashe-tashen hankula na addini da na kabilanci – tsakanin hare-haren ‘yan bindiga – sun faru a karamar hukumar Zangon Kataf, inda mutane 19 suka rasa rayukansu.

Mutane 12 ne kuma aka kashe a ƙaramar hukumar Sanga a cikin watanni ukun farko na shekarar 2023.

Yankin arewacin jihar ya shaida mutuwar mutane 38 a watanni ukun farko, inda aka samu mutuwar mutane 22 a karamar hukumar Zaria.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp