Home General Gwamnatin Tarayya ta Bayar da Hutun Sallah

Gwamnatin Tarayya ta Bayar da Hutun Sallah

Rauf

Gwamnatin Tarayya ta Bayar da Hutun Sallah

 

Gwamnatin Najeriya ta ayyana Juma’a 21 da Litinin 24 ga watan Afrilu a matsayin ranakun hutu don gudanar da shagulgulan bukukuwan ƙaramar sallah.

Ministan harkokin cikin gida na ƙasar Ogbeni Rauf Aregbesola, ne ya bayyana haka madadin gwamnatin tarayya.

Ministan ya kuma taya al’ummar musulman ƙasar murnar kammala azumin watan Ramadan.

Mista Aregbesola ya yi kira ga dukkan al’ummar musulmin ƙasar da su ci gba da ayyukan alkairin da suka koya a cikin watan na Ramadan.

Ya ce ”ina kira a gare ku da ku ci gaba da nuna wa juna halin dattaku, da soyayyar juna, da hakuri da juna da zaman lafiya da sadaukarwa da sauran kyawawan ayyuka, kamar yadda Annabi Muhammad SAW ya koya mana”.

Ana sa ran gudanar da bikin ƙaramar sallah tsakanin ranar Juma’a da Asabar a Najeriya, yayin da ake daf da kammala azumin watan Ramadan.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp