Home DUNIYA Saudiyya ta kwashe ƴan ƙasarta daga Sudan ciki har da ƴan Najeriya...

Saudiyya ta kwashe ƴan ƙasarta daga Sudan ciki har da ƴan Najeriya 10

Saudiyya ta bi sahun sauran ƙasashen duniya wajen kwashe ƴan ƙasarta daga Sudan a daidai lokacin da ake ci gaba da faɗa a ƙasar.

Cikin wata sanarwa da ofishin jakadancin Saudiyya a Najeriya ya fitar, ta ce ya zuwa yanzu ƙasar ta samu nasarar kwashe mutum 2, 544.

Sanarwar ta ce cikin mutanen, 119 sun ƙasance ƴan Saudiyya, yayin da 2,425 suka fito daga ƙasashe 74, inda goma daga cikin suka ƙasance ƴan Najeriya.

Ofishin jakadanci ya ce gwamnatin Saudiyya na yin duk mai yiwuwa wajen samarwa ƴan ƙasashen da aka kwashe duk abin da ya kamata, kafin mayar da su ƙasashensu na asali.

Har ila yau, ƙasar ta Saudiyya ta ce za ta yi iya kokarinta wajen ganin ta taimaka wa sauran ƙasashe kwashe mutanensu lami lafiya daga Sudan da kuma ganin an dakatar da faɗan da komawa kan tirba madaidaiciya a ƙasar.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp