Home DUNIYA Saudiyya ta kwashe ƴan ƙasarta daga Sudan ciki har da ƴan Najeriya...

Saudiyya ta kwashe ƴan ƙasarta daga Sudan ciki har da ƴan Najeriya 10

Saudiyya ta bi sahun sauran ƙasashen duniya wajen kwashe ƴan ƙasarta daga Sudan a daidai lokacin da ake ci gaba da faɗa a ƙasar.

Cikin wata sanarwa da ofishin jakadancin Saudiyya a Najeriya ya fitar, ta ce ya zuwa yanzu ƙasar ta samu nasarar kwashe mutum 2, 544.

Sanarwar ta ce cikin mutanen, 119 sun ƙasance ƴan Saudiyya, yayin da 2,425 suka fito daga ƙasashe 74, inda goma daga cikin suka ƙasance ƴan Najeriya.

Ofishin jakadanci ya ce gwamnatin Saudiyya na yin duk mai yiwuwa wajen samarwa ƴan ƙasashen da aka kwashe duk abin da ya kamata, kafin mayar da su ƙasashensu na asali.

Har ila yau, ƙasar ta Saudiyya ta ce za ta yi iya kokarinta wajen ganin ta taimaka wa sauran ƙasashe kwashe mutanensu lami lafiya daga Sudan da kuma ganin an dakatar da faɗan da komawa kan tirba madaidaiciya a ƙasar.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp