Sojojin Nijeriya sun hallaka ‘yan Ta’ addan 3 a jihar Zamfar

Dakarun sojin Najeriya karkashin Rundunar Operation HADARIN DAJI sun sami asarar hallaka ‘yan bindiga 3 a wani musayar wuta a dajin Gusau.

Wannan na kunshe ta cikin wata sanarwa mai dauke da sa hannun daraktan yada labarai na shalkwatar rundunar Manjo Janar Musa DANMADAMI.

Sanarwar mai dauke da kwana watan 30 ga wata Afrilu 2023, tace a wani aikin tarwatsa ‘yan bindiga rundunar ta tarwatsa gungun su na Anka ANKA, karkashin ikon DAN KAMFANI dake karamar hukumar Anka a jihar Zamfara.

Dakarun sojin sun yi arangama da’ yan bindiga inda suka hallaka 3 daga cikin su, tare da kwato bindiga kirar PKT guda 1, dauke da gidan Alburushi 48 masu tsayi mita 7.62 wanda ke dauke da Alburushin kwaya 54, sai bindiga kirar AK47 guda 3, sai kuma kunson Alburushin na musamman mai tsayi mita 7.62 da kuma baburan hawa 3.

Matakin babban iko na rundunar HADARIN DAJI ya yaba da aikin dakarun sojin, tare da neman Al’ummar gari su cigaba da basu hadin kai domin kakkabe ayyukan ‘yan ta’ addan a yankin.

PRNigeria hausa

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1190 days 9 hours 24 minutes 17 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1172 days 11 hours 5 minutes 42 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com