Home Labarai Sudan na gab da rugujewa -MDD

Sudan na gab da rugujewa -MDD

Majalisar Dinkin Duniya tace kasar Sudan na gab da rugujewa ganin yadda ake ci gaba da samun amon wuta da karar fashe fashe a birnin Khartoum, duk da tsawaita tsagaita wutar da bangarorin dake rikicin kasar suka sanar a jiya.

Tuni wannan rikici wanda ya shiga mako na 3 ya tilastawa dubban yan kasar Sudan tserewa zuwa kasashen makota irin su Masar da Chadi da kuma Jamhuriyar Afirka domin samun mafaka.

Akalla mutane sama da 500 aka tabbatar da mutuwar su a wannan rikici da ya barke tun daga ranar 15 ga watan jiya, tsakanin shugaban soji Janar Abdel Fateh al-Burhan da mataimakin sa kuma shugaban jami’an tsaron kai dauki na RSF, Mohammed Hmadan Daglo.

Miliyoyin mazauna birnin Khartum sun makale a cikin gidajen su yayin da suke fama da rashin abinci da kuma ruwan sha, yayin aka katse wutar lantarki, sai kuma jiragen yakin dake ci gaba da shawagi suna kai hare hare ba tare da kaukautawa ba.

Wakilin kamfanin dillancin labaran Faransa a Khartoum yace ko ayau litinin an ga jiragen yaki na shawagi a kudancin birnin, yayin da mayakan Daglo ke kai musu hari da makaman kakkabo jirage.

Kasashen duniya kuma sun mayar da hankali ne wajen kwashe mutanen su da wannan rikici ya ritsa da su, yayin da alkaluman Majalisar Dinkin Duniya suka nuna cewar ya zuwa yanzu an kwashe baki sama da 50,000.

Daliban Najeriya na cikin dubban yan kasashen waje da suke fatan ganin an mayar da su gida tun bayan barkewar rikicin, amma har ya zuwa wannan lokaci babu koda mutum guda da aka mayar gida.

Sai dai Babban sakatare a ma’aikatar jinkai ta Najeriya, Dr Nasir Sani Gwarzo yace sun sake fasalin kwashe daliban, kuma yanzu za suyi amfani da tashar Port Sudan ne.

Ya zuwa yanzu iyayen wadannan dalibai na cikin zulumi ganin yadda yakin ke ci gaba da kazancewa, yayin da kasashen duniya suka kasa shawo kan hafsoshin dake rikicin.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp