Home Labarai Mutum miliyan 4.3 za su yi fama da yunwa a jihohin Adamawa,...

Mutum miliyan 4.3 za su yi fama da yunwa a jihohin Adamawa, Borno da Yobe – MDD

Shirin Majalisar Ɗinkin Duniya na samar da abinci ya yi gargaɗin cewa akwai mutum miliyan 4.3 za su yi fama da matsananciyar yunwa a jihohin Adamawa da Borno da kuma Yobe, dukkansu a yankin arewa maso gabashin Najeriya.

Shirin ya bayyana hakan ne cikin wata sanarwa da ya fitar, game da wani rahoto da ya tattara kan matsananciyar yunwa a yankin ƙasashen kudu da hamadar Sahara.

Shirin na WFP ya nuna damuwa kan rikicin da aka kwashe shekaru ana yi da ‘yan bindiga zai iya jefa Najeriya cikin yunwa da tamowa, yayin da miliyoyin mutane suka dogara kan taimako da ake ba su na abinci, wanda kuma suke fuskantar barazanar faɗawa cikin yunwa.

“Kimanin mutum 600,000 na kan gabar faɗawa cikin wannan musifa.

Mutane za su fuskanci yanayin neman ɗaukin gaggawa saboda ƙarancin abinci, za kuma a fuskanci mummunar matsalar tamowa da mace-mace saboda ƙarancin kai kayan agaji,” in ji shirin.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp