Home DUNIYA Burkina Faso: Adadin mutanen da aka kashe a Karma ya kai 136

Burkina Faso: Adadin mutanen da aka kashe a Karma ya kai 136

Wata kungiyar kare hakkin dan adam a Burkina Faso ta ce adadin fararen hula da aka kashe a kauyen Karma da ke yankin arewacin Burkina Faso a ranar 20 ga watan afrilun nan, ya kai 136, cikinsu akwai mata 50 da kananan yara 21.

Kididdigar da kungiyar ta fitar a ranar juma’a da ta gabata game da kisan ya kuma nuna jarirai 30, ‘yan kasa da wata 1 na daga cikin wadanda mayakan suka kashe.

Wasu ‘yan bindiga sanye da kayan soji ne suka farwa kauyen, inda  suka yi wa mutane da dama kisan gilla, harin da ke zuwa bayan wanda wasu mayaka masu ikirarin jihadi suka kai wani wuri kusan da kauyen Karma a ranar 15 ga watan Afrilun nan inda suka kashe sojoji 6 da wsu 34.

Kungiyar ta kuma ce baya ga wadannan, maharan sun kuma farwa wasu kauyuka na daban, inda suka kashe mutane 6 a kauyen Dinguiri, wasu 2 a Ménè, sannan suka kashe wasu mutanen 3 a kan hanyar dake tsakanin kauyukan Ouahigouya da Barga.

Adadin mamatan da alkalin Ouahigouya dake yankin arewacin kasar ya sanar a ranar lahadi na nuna kusan mutane 60 aka kashe a mabanbantan hare haren, saidai mazauna kauyen Karma da wasu shaidun gani da ido sun ce adadin ya zarce 100.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp