‘Yan sanda sun kama matashin da ake zargi ya kashe mahaifiyarsa a Kano

Rundunar ƴan sanda a jihar Kano sun sanar da kama matashin nan Ibrahim Musa da ake zargi ya hallaka mahaifiyarsa a Kano.

A wani sako da kakakin rundunar ƴan sandan jihar SP Abdullahi Haruna Kiyawa ya fitar, ta ce an kama matashin ne a maɓoyarsa da ke karamar hukumar Dawakin Tofa na jihar ta Kano.

Kiyawa ya ce matashin ya amsa laifin da ake zarginsa da shi, inda kuma ya ce yana tu’ammali da ƙwayoyi masu sa maye.

A yanzu dai za a tura shi zuwa kotu bayan kammala bincike.

A jiya ne dai aka ruwaito cewa matashin ya caccaka wa mahaifiyarsa mai shekara 50 wuƙa a kanta da ƙirjinta da kuma sauran sassan jiki, inda ya tsere bayan aikata laifin.

PRNigeria hausa

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1190 days 23 hours 28 minutes 3 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1173 days 1 hour 9 minutes 28 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com