Rundunar ƴan sanda a jihar Kano sun sanar da kama matashin nan Ibrahim Musa da ake zargi ya hallaka mahaifiyarsa a Kano.
A wani sako da kakakin rundunar ƴan sandan jihar SP Abdullahi Haruna Kiyawa ya fitar, ta ce an kama matashin ne a maɓoyarsa da ke karamar hukumar Dawakin Tofa na jihar ta Kano.
Read Also:
Kiyawa ya ce matashin ya amsa laifin da ake zarginsa da shi, inda kuma ya ce yana tu’ammali da ƙwayoyi masu sa maye.
A yanzu dai za a tura shi zuwa kotu bayan kammala bincike.
A jiya ne dai aka ruwaito cewa matashin ya caccaka wa mahaifiyarsa mai shekara 50 wuƙa a kanta da ƙirjinta da kuma sauran sassan jiki, inda ya tsere bayan aikata laifin.
PRNigeria hausa
Kidnapped School Children
Yauri FGC Students, Kebbi1462 days 18 hours 33 minutes 16 seconds,
Baptist School Students, Kaduna
1444 days 20 hours 14 minutes 41 seconds
Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021
Report By: PRNigeria.com