Home DUNIYA ECOWAS ta sake yin kiran a murkushe ta’addancin da ke karuwa a...

ECOWAS ta sake yin kiran a murkushe ta’addancin da ke karuwa a tsakiyar Sahel

Ƙungiyar Raya Tattalin Arziƙin Ƙasashen Afirka ta Yamma (ECOWAS) ta jaddada buƙatar a ɗauki matakan gaggawa domin magance ƙaruwar hare-haren ta’addanci a tsakiyar Sahel.

Kwamishinan ECOWAS da ke kula da harkokin siyasa da zaman lafiya da tsaro, Ambasada AbdelFateh Moussa ne ya yi wannan kira a wani taron bayar da horo na yini biyar.

An yi wa taron taken Tabbatar da ci gaban zaman lafiya: Rawar ƴan sanda da jami’an Jandarma wajen tafiyar da ayyukan ECOWAS wajen wanzar da zaman lafiya.

ECOWAS ce ta shirya taron haɗin gwiwa da kwalejin horas da ƙananan jami’an soji ta Najeriya tare da tallafin shirin ECOWAS kan zaman lafiya da tsaro.

Moussa ya ce ayyukan wanzar da zaman lafiya da aka saba na zama tsohon yayi saboda yanayin rikici a yankin.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp