Home Labarai Kamfanin NNPC ya ƙara farashin man fetur a Najeriya

Kamfanin NNPC ya ƙara farashin man fetur a Najeriya

Kamfanin man fetur na Najeriya ya tabbatar da cewa ya ƙara kuɗin litar mai a ƙasar.

A wata sanarwa da ta kamfanin ya wallafa a shafinsa na twitter, kamfanin ya ce ya yi ƙarin farashin domin yin daidai da halin da ake ciki.

Kuma ya roƙi afuwa kan wahalhalun da hakan zai iya haifarwa.

Hakan dai na zuwa ne bayan shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu ya sanar, a lokacin rantsar da shi cewa gwamnati ta dakatar da tallafin.

Tun bayan furucin sabon shugaban ƙasar ne aka fara ganin dogayen layuka a gidajen mai, yayin da kowane gidan mai ke sayar da man a farashi daban-daban.

Ita ma, Ƙungiyar Dillalan Man Fetur masu Zaman Kansu ta Najeriya (IPMAN), ta fitar da sabon farashin da gidajen mai za su rinƙa sayar da litar mai a faɗin ƙasar.

A cewar ƙungiyar, ta ɗauki matakin ne bayan da Kamfanin Man Fetur na Ƙasar (NNPC) ya miƙa mata nasa sabon farashin.

Shugaban ƙungiyar reshen Arewa, Bashir Ɗanmalan wanda ya tabbatar wa BBC da ƙarin, ya ce yanzu farashin zai kama ne daga naira 500 zuwa 600, dangane da yankin ƙasar.

Dama dai farashin man fetur ya tashi a sassa daban-daban na ƙasar tun bayan furucin sabon shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinu, wanda ya ce “Tallafin man fetur ya tafi.”

An rinƙa samun dogayen layukan ababen hawa a gidajen mai, inda farashin lita ya rinƙa tashi babu ƙaƙautawa.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp