Home SIYASA Yan Majalisar Wakilan Najeriya sun goyi bayan Tinubu kan cire tallafin mai

Yan Majalisar Wakilan Najeriya sun goyi bayan Tinubu kan cire tallafin mai

‘Yan Majalisar Wakilan Najeriya sun yaba wa yunƙurin gwamnatin Shugaba Bola Tinubu na tabbatar da janye tallafin man fetur.

Sun ɗauki matakin ne bayan gabatar da ƙudirin gaggawa da ɗan majalisa Jimoh Olajide ya yi a zamanta na yau Talata.

Sakamakon haka ne Majalisar ta nemi ‘yan Najeriya da su yi haƙuri tare da yi wa gwamnati addu’a game da matakin.

A ranar Litinin ne – a jawabinsa na rantsuwar kama aiki – Shugaba Tinubu ya ce “tallafin man fetur ya ƙare”, yana mai cewa babu tanadin kuɗin a kasafin kuɗi na wata shidan ƙarshe na 2023.

Tuni jawabin nasa ya janyo dogayen layuka a gidajen mai a faɗin ƙasar, inda mutane ke rige-rigen sayen man.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp