Home SIYASA Yan Majalisar Wakilan Najeriya sun goyi bayan Tinubu kan cire tallafin mai

Yan Majalisar Wakilan Najeriya sun goyi bayan Tinubu kan cire tallafin mai

‘Yan Majalisar Wakilan Najeriya sun yaba wa yunƙurin gwamnatin Shugaba Bola Tinubu na tabbatar da janye tallafin man fetur.

Sun ɗauki matakin ne bayan gabatar da ƙudirin gaggawa da ɗan majalisa Jimoh Olajide ya yi a zamanta na yau Talata.

Sakamakon haka ne Majalisar ta nemi ‘yan Najeriya da su yi haƙuri tare da yi wa gwamnati addu’a game da matakin.

A ranar Litinin ne – a jawabinsa na rantsuwar kama aiki – Shugaba Tinubu ya ce “tallafin man fetur ya ƙare”, yana mai cewa babu tanadin kuɗin a kasafin kuɗi na wata shidan ƙarshe na 2023.

Tuni jawabin nasa ya janyo dogayen layuka a gidajen mai a faɗin ƙasar, inda mutane ke rige-rigen sayen man.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp