Home Labarai Kamfanin NNPC ya ƙara farashin man fetur a Najeriya

Kamfanin NNPC ya ƙara farashin man fetur a Najeriya

Kamfanin man fetur na Najeriya ya tabbatar da cewa ya ƙara kuɗin litar mai a ƙasar.

A wata sanarwa da ta kamfanin ya wallafa a shafinsa na twitter, kamfanin ya ce ya yi ƙarin farashin domin yin daidai da halin da ake ciki.

Kuma ya roƙi afuwa kan wahalhalun da hakan zai iya haifarwa.

Hakan dai na zuwa ne bayan shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu ya sanar, a lokacin rantsar da shi cewa gwamnati ta dakatar da tallafin.

Tun bayan furucin sabon shugaban ƙasar ne aka fara ganin dogayen layuka a gidajen mai, yayin da kowane gidan mai ke sayar da man a farashi daban-daban.

Ita ma, Ƙungiyar Dillalan Man Fetur masu Zaman Kansu ta Najeriya (IPMAN), ta fitar da sabon farashin da gidajen mai za su rinƙa sayar da litar mai a faɗin ƙasar.

A cewar ƙungiyar, ta ɗauki matakin ne bayan da Kamfanin Man Fetur na Ƙasar (NNPC) ya miƙa mata nasa sabon farashin.

Shugaban ƙungiyar reshen Arewa, Bashir Ɗanmalan wanda ya tabbatar wa BBC da ƙarin, ya ce yanzu farashin zai kama ne daga naira 500 zuwa 600, dangane da yankin ƙasar.

Dama dai farashin man fetur ya tashi a sassa daban-daban na ƙasar tun bayan furucin sabon shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinu, wanda ya ce “Tallafin man fetur ya tafi.”

An rinƙa samun dogayen layukan ababen hawa a gidajen mai, inda farashin lita ya rinƙa tashi babu ƙaƙautawa.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp