Home Labarai Kamfanin NNPC ya ƙara farashin man fetur a Najeriya

Kamfanin NNPC ya ƙara farashin man fetur a Najeriya

Kamfanin man fetur na Najeriya ya tabbatar da cewa ya ƙara kuɗin litar mai a ƙasar.

A wata sanarwa da ta kamfanin ya wallafa a shafinsa na twitter, kamfanin ya ce ya yi ƙarin farashin domin yin daidai da halin da ake ciki.

Kuma ya roƙi afuwa kan wahalhalun da hakan zai iya haifarwa.

Hakan dai na zuwa ne bayan shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu ya sanar, a lokacin rantsar da shi cewa gwamnati ta dakatar da tallafin.

Tun bayan furucin sabon shugaban ƙasar ne aka fara ganin dogayen layuka a gidajen mai, yayin da kowane gidan mai ke sayar da man a farashi daban-daban.

Ita ma, Ƙungiyar Dillalan Man Fetur masu Zaman Kansu ta Najeriya (IPMAN), ta fitar da sabon farashin da gidajen mai za su rinƙa sayar da litar mai a faɗin ƙasar.

A cewar ƙungiyar, ta ɗauki matakin ne bayan da Kamfanin Man Fetur na Ƙasar (NNPC) ya miƙa mata nasa sabon farashin.

Shugaban ƙungiyar reshen Arewa, Bashir Ɗanmalan wanda ya tabbatar wa BBC da ƙarin, ya ce yanzu farashin zai kama ne daga naira 500 zuwa 600, dangane da yankin ƙasar.

Dama dai farashin man fetur ya tashi a sassa daban-daban na ƙasar tun bayan furucin sabon shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinu, wanda ya ce “Tallafin man fetur ya tafi.”

An rinƙa samun dogayen layukan ababen hawa a gidajen mai, inda farashin lita ya rinƙa tashi babu ƙaƙautawa.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp