Home Labarai Gwamnatin Borno za ta ɗauki malamai 5,000 aiki da dawo da karatun...

Gwamnatin Borno za ta ɗauki malamai 5,000 aiki da dawo da karatun yamma

Gwamnar jihar Borno, Babagana Zulum ya ce za a dauki malamai 5,000 aiki don fara karatun firamare da sakandare da rana domin magance matsololin cunkoso da kuma rage yawan yaran da ba sa zuwa makaranta.

Zulum ya bayyana hakan ne a ranar Litinin a Maiduguri yayin jawabinsa na farko bayan rantsar da shi karo na biyu.

Ya ce : “Duk da cewa mun gina sabbin makarantu masu girman gaske tare da fadada makarantun da ake da su da sabbin ajujuwa kusan 1,000, amma har yanzu muna fuskantar matsalar cunkoso a ajujuwa, kuma muna fama da matsalar da dubban yara da ba sa zuwa makaranta”

“Ina mai farin cikin sanar da cewa nan ba da jimawa ba jihar Borno za ta fara tsarin makarantun firamare da sakandare na rana. Na nada kwamitin aiwatarwa da zai tsara hanyoyin da za a fara karatun makarantun la’asar, kuma zai tantance makarantun gwajin da za a zabo daga wasu manyan makarantunmu na Maiduguri da ke da lantarki.”

Zulum ya bayyana cewa bullo da tsarin karatun na yamma zai bukaci karin ma’aikata, don haka ya umurci ofishin shugaban ma’aikata da ya zakulo wasu kwararrun ma’aikatan da a halin yanzu ba sa aiki a sakatariyar gwamnati, wadanda za a horar da su kan sanin makamar aikin.

Gwamnan ya kuma ce za a dauki matakan tsaro domin tabbatar da samun nasarar makarantun na yamma, yana mai cewa a wasu lokutan ana iya daukar darasi har zuwa farkon dare.

Zulum ya ce za a sake bullo da wasu matakai kamar jarrabawar gwaji da ake kira ”Mock” da Ingilishi a makarantun sakandare tare da kafa cibiyoyi daukar jarrabawa masu inganci ta yadda gwamnati za ta iya gano baiwa da fasihar yaran.

 

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp