Sabon Gwamnan kano ya fara Rusau

Zababben gwamnan jihar Kano Engr Abba Kabir Yusuf ya jagoranci rushe wasu gine gine da aka yi a kewayen filin sukuwa dake unguwar Nassarawa.

Abba Kabir da sauran mukarraban gwamnati Hadi da jami’an tsaro sun Isa wajen ne da misalin karfe 1 da minti 30 na Daren Asabar, Kuma an rushe wasu muhimman sassa na gine-ginen Nan take.

Idan za’a iya tuna tun bayan samun Nasara a zaben gwamnoni na 2023 Gwamnan kanon ya shawarci masu gine gine a filayen gwamnatin jihar dasu dakata.

Sai dai ana kallon wannan aiki kai tsaye wani mataki ne na dawo da dukiyoyin gwamnatin da aka sayar ba bisa ka’ida ba.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com