Home Labarai Sabon Gwamnan kano ya fara Rusau

Sabon Gwamnan kano ya fara Rusau

Zababben gwamnan jihar Kano Engr Abba Kabir Yusuf ya jagoranci rushe wasu gine gine da aka yi a kewayen filin sukuwa dake unguwar Nassarawa.

Abba Kabir da sauran mukarraban gwamnati Hadi da jami’an tsaro sun Isa wajen ne da misalin karfe 1 da minti 30 na Daren Asabar, Kuma an rushe wasu muhimman sassa na gine-ginen Nan take.

Idan za’a iya tuna tun bayan samun Nasara a zaben gwamnoni na 2023 Gwamnan kanon ya shawarci masu gine gine a filayen gwamnatin jihar dasu dakata.

Sai dai ana kallon wannan aiki kai tsaye wani mataki ne na dawo da dukiyoyin gwamnatin da aka sayar ba bisa ka’ida ba.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp