Home Labarai NLC DA TUC sun fasa shiga yajin aiki

NLC DA TUC sun fasa shiga yajin aiki

Rahotannin daga Nijeriya na bayyana cewa Manyan kungiyoyin kwadago biyu a kasar na NLC da TUC sun jingine aniyarsu ta shiga yajin aikin sai baba-ta-gani wanda suka shirya farawa ranar Laraba kan tashin farashin man fetur.

Kungiyoyin biyu sun yanke wannan shawarar ce bayan ganawar da suka yi da bangaren gwamnatin tarayya a fadar shugaban kasa, ranar Litinin.

A makon da ya gabata ne dai kungiyoyin kwadago na Najeriya suka bai wa gwamnatin kasar wa’adin zuwa ranar Talata 6 ga watan Mayu domin ta janye cire tallafin man fetur ko kuma su tsunduma yajin aiki.

Shugaban Majalisar Wakilan Najeriya, Femi Gbajabiamila ne ya sanar da matsayar, wadda shugaban kungiyar kwadago ta kasa NLC, Joe Ajero ya tabbatar, bayan kwashe kimanin sa’oi shida ana tattaunawa tsakanin bangarorin biyu.

Wata sanarwar da shugabannin NLC da TUC suka sanyawa hannu, ta ce daya daga cikin dalilan jingine yajin aikin shi ne bai wa gwamnatin tarayya da bangaren ‘yan kwadago damar kafa wani kwamiti da zai duba batun yin karin albashin ma’aikata da kuma lokacin da za a aiwatar da tsarin.

Haka nan kuma za a duba tsarin bayar da tallafin kudade na Bankin Duniya ta yadda za a sanya masu karanin karfi a ciki.

Daga nan kungiyar kwadagon da gwamnati za su sake duba tsarin gyaran matatun man fetur na kasar ta yadda za a iya kammala gyara su.

Bugu da kari gwamnati za ta samar da tsarin gyara hanyoyin mota da kuma samar da layukan dogo a fadin kasar.

A karshe sanarwar ta ce kungiyar kwadago za ta sake yin wani zama da gwamnatin tarayya a ranar 19 ga watan Yuni domin samar da matsaya kan yadda za a aiwatar da tsare-tsaren da aka cimma.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp