Home Labarai NLC DA TUC sun fasa shiga yajin aiki

NLC DA TUC sun fasa shiga yajin aiki

Rahotannin daga Nijeriya na bayyana cewa Manyan kungiyoyin kwadago biyu a kasar na NLC da TUC sun jingine aniyarsu ta shiga yajin aikin sai baba-ta-gani wanda suka shirya farawa ranar Laraba kan tashin farashin man fetur.

Kungiyoyin biyu sun yanke wannan shawarar ce bayan ganawar da suka yi da bangaren gwamnatin tarayya a fadar shugaban kasa, ranar Litinin.

A makon da ya gabata ne dai kungiyoyin kwadago na Najeriya suka bai wa gwamnatin kasar wa’adin zuwa ranar Talata 6 ga watan Mayu domin ta janye cire tallafin man fetur ko kuma su tsunduma yajin aiki.

Shugaban Majalisar Wakilan Najeriya, Femi Gbajabiamila ne ya sanar da matsayar, wadda shugaban kungiyar kwadago ta kasa NLC, Joe Ajero ya tabbatar, bayan kwashe kimanin sa’oi shida ana tattaunawa tsakanin bangarorin biyu.

Wata sanarwar da shugabannin NLC da TUC suka sanyawa hannu, ta ce daya daga cikin dalilan jingine yajin aikin shi ne bai wa gwamnatin tarayya da bangaren ‘yan kwadago damar kafa wani kwamiti da zai duba batun yin karin albashin ma’aikata da kuma lokacin da za a aiwatar da tsarin.

Haka nan kuma za a duba tsarin bayar da tallafin kudade na Bankin Duniya ta yadda za a sanya masu karanin karfi a ciki.

Daga nan kungiyar kwadagon da gwamnati za su sake duba tsarin gyaran matatun man fetur na kasar ta yadda za a iya kammala gyara su.

Bugu da kari gwamnati za ta samar da tsarin gyara hanyoyin mota da kuma samar da layukan dogo a fadin kasar.

A karshe sanarwar ta ce kungiyar kwadago za ta sake yin wani zama da gwamnatin tarayya a ranar 19 ga watan Yuni domin samar da matsaya kan yadda za a aiwatar da tsare-tsaren da aka cimma.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp