Home Labarai Tinubu na ganawa da Gwamnonin Nijeriya

Tinubu na ganawa da Gwamnonin Nijeriya

Shugaban Najeriya Bola Tinubu na ganawa da gwamnonin jihohin kasar 36 a fadar gwamnatin ƙasar da ke Abuja.

Wannan ce ganawar shugaban ta farko da ƙungiyar gwamnonin ƙasar ƙarƙashin jagorancin gwamnan jihar Kwara AbdulRahman AbdulRazaq tun bayan hawansa karagar mulki a makon da ya gabata.

To amma a ranar Juma’ar da ta gabata shugaban ƙasar ya gana da wasu gwamnoni a ƙarƙashin ƙungiyar gwamnonin jam’iyyar APC mai mulki

Daga cikin masu halartar ganawar akwai mataimakin shugaban ƙasar Sanata Kashim Shettima da sakataren gwamnatin tarayya Sanata George Akume, da mai bai wa shugaban ƙasa shawara kan harkokin tsaro Manjo Janar Babagana Monguno mai ritaya, da sauran jami’ai.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp